ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin Buhari Ga Jami’an Tsaro Na Kawo Karshen ‘Yan Ta’adda

by Aisha Seyoji
4 years ago
Jami'an tsaro

A yau mun kawo ra’ayoyinku ne a kan wa’adin zuwa ranar 31 ga watan Disamba da Shugaba Buhari ya ba jami’an tsaron na su kawo karshen ayyukan ta’addanci a Nijeriya. Shin akwai yiwuwar cimma wannan wa’adin kuwa? Ga bayanan da mas bibiyar ska yi

Comr Isma’il Ibrahim Gusau
Wannan labarin mun saba jinshi ga bakin shugaban kasa da manyan masu ruwa da tsaki a kan sha’anin tsaro, ba’a biyo hanyar magance matsalar tsaro ba a Nijeriya, tayaya za a ce dan ta’adda yafi gwamnati mallakar makamai kaga harkar tsaron kasar nan akwai lauje cikin nadi.

Kuma idan ka duba ko yaushe magana daya ce suke yi wa ‘yan kasa babu wani sauyi da ake samu itace tun yana danye ake lankwasa shi, amma yanzu kam sunyi sake, duk abinda baka gyara ba shekara bakwai da rabi yanzu wane gyara akeso ayi. Allah dai ya zaba muna shugabanni nagari.

ADVERTISEMENT

Muhd Basheer Sa’ad
An dade ana ruwa kasa tana shanyewa! Kawo yanzun dai mun san wannan magana ta Shugaban Buhari kanzon kurege ce.
Domin kuwa a baya ya fadi hakan kuma babu abunda ya sauya. Abunda ya kamata kawai mu mika al’amuran mu ga Ubangiji kawai domin shi ne zai yi mana maganin su.

Abubakar Mohammed Joda
Muna fatan alkhairi a kullum ga jami’an tsaronmu, muna kuma addu’ar Allah ya kawo mana karshen ta’addanci a yankunanmu. Amma dai karya da farfagandar gwamnatin nan babu wanda bai ganeshi ba izuwa yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Real Miftahu Ahmad Panda
Ni dai ina ganin, abu ne mawuyaci hakan ya iya yiwuwa (ma’ana a iya kawo karshen ayyukan ta’addanci, a cikin wannan wa’adi), duba da yadda a baya ma, shugaban ya sha bada irin wannan umarni ga hafoshin tsaron kasar nan, amma shiru ka ke ji. Sai dai kuma, ba ma ce mun yanke kauna baki daya da yiwuwar hakan ba.

Fatan mu dai, Allah ya kawo mana karshen wadannan matsalolin tsaro da su ka ta’azzara, musamman ma a yankin Arewacin Nijeriya.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
Ai ko wanda ba dan Nijeriya ba idan ya samu wannan labari ya san cewa abu ne da ba zai yiwu ba.

Balle mu da ke rayuwa cikin kasar kuma yankunan da ta’addancin ya ke faruwa.
Maganar Gaskiya ko da Buharin da kansa zai fito ya yi aikin tare da Jami’an tsaro ina mai tabbatar miki da cewa ba za a iya kawo karshen abin a wa’adin da aka diba ba.
Abin da ya fi dacewa da mu shi ne Addu’a. Allah ya kawo mana karshen wannan ta’addanci ya ba mu shuwagabanni na gari. Wanda za su nuna jin zafin abin ta yadda za a magance matsalar.

Khadija Muhammad
Da ikon Allah mu kasance masu fatan nasara ba màganganun banza ba

Mohammed Inuwa
Wannan mataki da Shugaban Kasa ya dauka ya yi daidai. Domin kadan akwi kayan aiki da hakan zai yiwu InshaaAllah. Kuma muna addu’a da kara bawa gwamnati hadin kai. Allah kawo kasarmu zaman lafiya.

Comr Hassan S Umar
Idan kin san abinda ake cewa shifcin Gizo! To wannan shi ne Shifcin Gizo, magance matsalar tsaro yana daya daga cikin 3 majors na abubuwan da suka kafa gwamnatin Buhari A 2015 saboda tsananin takura da harin ‘yan ta’adda a Nijeriya musamman Arewa. Amma gashi yau shekara kusan 8, an kusa kamala wa’adi na biyu amma.

Kar ku manta a wannan gwamnatin aka samu kungiyar ikirarin jihadi ta (ISWAP) a yankin arewa maso gabas.
Kar ku manta a wannan gwamnatin aka samu harkokin garkuwa da mutane a yankin arewa maso yamma da arewa ta tsakiya, haka kuma a wannan lokacin ne aka samu ayyukan ‘yan tawayenh Biyafra ya kara karuwa. Muna dai rokon Allah ya taimaka wa jami’antsraomu donj su samju nasarar da ake bukata a kan ayyukan ‘yanta’adda a sassan Nijeriya

Sulaiman Muhammad
Gaskiya mai girma shugaban kasa yasha fadin haka saboda babu wani abu da zai canza.
Domin matsalar tsaron Nijeriya akwai Turawan yamma da Amurka da ‘yan Nijeria da masu mulkin Nijeria duk sun san komai basu yi niyar gyaran ba ne

Widad Isma’il
Allah ya basu ikon aiwatar da abinda zamu yi masu shi ne addua, amma gaskiya al’amarin tsaro abin dubawa ne tunda har za a iya kamo wanda suke cin zarafin manya a hukuntasu, a ganina kamo wadanda suke ta’addanci binciko su abu me sauki, inda gaske ake yi.

Jami'an tsaro
Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Jami'an tsaro

Gwamnatin Kano Ta Kulla Yarjejeniya Da Makarantar Morocco Kan Harkar Noma

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.