• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku Kan Tasirin Amfani Da Kudi A Siyasar 2023

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Siyasa
0
kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barkanmu da sake saduwa a wannan fili,a wannan mako mun kawo ra’ayoyinku a kan yadda ‘yan siyasa ke amfani da kudi wajen jan hankalin talakawa masu jefa kuri’a.

Da kuma jan hankalin masu kada kuri’a domin ganin sun yi amfani da cancanta sun zabi mutanen da za su yi musu aiki ba tare da la’akari da masu basu kudi ba a zaben 2023.

Muhd Basheer Sa’ad
Ni bana ganin laifin ‘yan siyasa a wannan lamarin saboda mafiyawancin su kasuwanci suka dauki siyasar su. Saboda haka sun saka kudi sun sayi kuri’a dole ne suyi yadda suka ga dama da talakawa tunda sun sayi ‘yancin su ne da kudi.

Don haka dole masu kasa kuri’u su hankalta da karba kudi yayin zabe saboda idan har ka yarda ka amshi kudi kuma ka zabi mutum to shakka babu ka sayar da ‘yancin ka kuma babu yadda zakai dole sai abinda ka gani

Yusuf Muhammad Jalingo
Kowanne talaka yanzu abinda yake cewa “Allaah ya zaba mana shugaba nagari” sabida jiki magayi don kowa yaji ajikinsa.
Matsalar shi ne talauci ne aka sakawa mutane na dole shi ne su kuma masu neman mulki ido a rufe suke amafani da wannan daman sai mukuma talakawa muke karba amma badon anason hakan ba.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Muna amfani da wannan dama wajen yi wa al’umma tuni a kan kar asake zaben tumun dare don duk me yin zabe atunanin zai iya banbance abu mai kyau da maras kyau.
Allaah ya zaba mana shugabanni nigari. Amiin

Baban Khairat
A Ra’ayi na kamata ya yi mutane (ordinary masses) su yi hakuri da yanayin da aka samu kai su duba chanchantan dantakara da za su zaba, Abin ban haushinma shi ne wai bayan shekaru hudu lokacin zabe kaga, ana raba wa mutane abinda ko abinci na ranan ba zai isheka watakila ba laifin masu zaben ba ne halin talauci da tsadar rayuwa ne, Amma kuma bashi zai sa kasa yarda ‘yancin kaba, fatanmu dai shi ne Allah ya bamu sa ar shugabannin na gari,

Mahdee Bashir
Duk wanda ya karbi kudi a wajen ‘yan siyasa kuma ya zabe shi to ya tabbata ya sayar da ‘yancinsa da ta al’ummarsa, fakat!!!

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya wannan ba abune mai kyau ba, muna kira ga ‘yan siyasarmu da su gyara idai har gyaran ake so ayi.

It’z Jameel Moh’d
Kawai Allah ya bamu shugaba nagari amma dai duk wanda ya cire kudi ya sayi delegate sannan ya sayi talakawa saboda su zabe shi, Wallahi inya ci zabe ba zai mana aiki ba, yakamata mu yi amfani da hankalin mu wajen zaben shugaba na gari

Yahaya Aliyu Sani
To mu dai munsan da cewa talaka baida wani katabus, Allah ya zaba mana mafi alheri

Nazifi Haruna Iliyasu
To idan bera da sata daddawa ma da wari, matsalar da aka samu shi ne har yanzu tallaka bai san kansa ba, da yasan kansa da an samu saukin al’amurra, to abinda nake gani Idan har dan siyasa zai baka dan abinda bai taka kara ya karya ba ka zabe shi tofa duk yadda ya yi dakai daidai ne domin kuwa ba don Allah ka zabe shi ba, kudi ya biya ka, to amma da yake mafi a’ala ga tallaka shi ne ya cire kwadayi ya zabi wanda ya chanchanta.

Widad Isma’il
Ai gani ga wanne ya ishi wane tsoron Allah, ai ko wannan jarrabawar wannan gwamnati ya kamata mutane su san su waye su kwadayi a lasa maka zuma a baki zakin sa na dan lokaci zai bace maka a baki amma abin da zai biyo baya da kanka zaka kai wa kanka hisabi ba sai an kai ga gaci ba.

Sulaiman Muhammad
Gaskiya har yandu talakawa masu jefa kuri’a kunnansu bai yi laushi ba, tun kafin ranar zabe an fara basu omo da indome

Adamu Yunusa Ibrahim
Fatan alheri.

Hussein B Gama
Yanzu kam lamarin sai dai mubi da innalillahi saboda komai ya lalace


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Ta’adda Da Dama Sun Mutu A Wata Arangama Tsakanin ISWAP Da Boko Haram A Borno

Next Post

Matar Da Ta Sheka Wa Matashi Tafasasshen Ruwan Shayi Ta Shiga Hannun ‘Yansanda A Kano

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

1 day ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

1 day ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

4 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

7 days ago
Next Post
Matar Da Ta Sheka Wa Matashi Tafasasshen Ruwan Shayi Ta Shiga Hannun ‘Yansanda A Kano

Matar Da Ta Sheka Wa Matashi Tafasasshen Ruwan Shayi Ta Shiga Hannun 'Yansanda A Kano

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.