Shekaru 10 da suka gabata, Rahama Sadau ta fito a cikin shirinta na farko a masana’antar Kannywood mai suna ‘Gani Ga Wane’, inda ta fito a matsayin jaruma mai tasowa a wancan lokacin. Tun daga wancan lokacin ne jarumar ta fito a fina-finai fiye da 100 da suka hada da wadanda ta fito a masana’antun shirya fina -finai na Nollywood na Nijeriya da kuma Bollywood ta kasar Indiya.
Jarumar wadda ta samu kwalin karatun digirin-digirgir a jami’ar Eastern Mediterranean Unibersity da ke Arewacin Cyprus, tana daga cikin jaruman da suka kware wajen magana da harsunan duniya daban-daban da suka hada da Turanci, Indiyanci, larabci da kuma Hausa cikin natsuwa da kwarewa, Jarumar ta samu nasarori da dama a cikin shekarun da ta kwashe tana harka ta shirin fim, ta zama mace ta farko a tarihi a masana’antar Kannywood da ta samu shiga manyan fina-finan kasar Indiya na Bollywood, daga cikin manyan fina-finan da ta fito akwai Khuda Haafiz, inda ta fito tare da jarumin Bollywood, Bidyut Jammwal da Up North, Sons Of The Caliphate, Postcards da sauran makamantansu.
- Kabilar Bayankole Da Innar Amarya Ke Jima’i Da Ango Domin Gwaji
- Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa
Sadau ta zama gwarzuwar jarumar Kannywood a shekarar 2014, bayan da ta fito a wani shiri mai suna ‘Sabuwar Sangaya’, bayan nan ta fito a manyan fina-finan Kannywood kamar ‘Mati Da Lado’, Rariya da Rumana.
Ranar 3 ga Oktoba 2016, kungiyar shirya fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN), ta dakatar da ita daga shiga duk wata harka ta kannywood, saboda fitowar da ta yi a wani faifan bidiyo na soyayya tare da mawaki, Classik K, amma a watan Janairu 2018 ne aka dage haramcin da aka sa mata sakamakon sa hannun da gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya yi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp