• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoton Tattalin Arzikin Afirka Na 2023 Ya Nuna Nahiyar Na Bukatar Garambawul

by Leadership Hausa
2 years ago
in Tattalin Arziki
0
Rahoton Tattalin Arzikin Afirka Na 2023 Ya Nuna Nahiyar Na Bukatar Garambawul
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin ne, hukumar kula da tattalin arzikin Afirka ta Majalisar Dinkin Duniya (UNECA), ta gabatar da Rahoton Tattalin Arziki na Afirka a 2023 (ERA 2023) inda ya bayyana cewa, akwai bukatar yin kwarya-kwaryan gyaran fuska domin samun ci gaba mai dorewa da kuma jajircewa don cimma nasarar da ake fatan gani.

Daga cikin abubuwan da rahoton ya ce ya kamata a mayar da hankali a kai akwai bukatar kasashen yankin su gano hanyoyin da za su yi hadin kai da aiki da sahihan dabaru na habaka harkokin masana’antu.

Rahoton mai taken: “Gina gurbin Afirka da ya dace wajen bunkasa tattalin arzikin duniya”, wanda Darakta mai kula da harkokin tattalin arziki da mulki a hukumar (UNECA), Adam Elhiraika, ya gabatar, ya nuna cewa, tsarin ci gaban tattalin arzikin duniya a halin yanzu yana ba da mamaki ga kasashen Afirka bisa yadda suke da bukatar hanzarta habaka masana’antu ta hanyar yin gwaji da kyau kan abin da zai fi zama mafita gare su da kuma yadda za su daidaita lamarin bisa tsarinsu na gida.

  • NIS Reshen Ribas Ta Yi Wa Jami’ai Ado Da Sabbin Mukamai Da Kaddamar Da Sabbi

Elhiraika ya bayyana cewa, ci gaban da ake samu a Afirka yana da alaƙa da fitar da kayayyaki, yin aiki da manyan kasashen duniya da kamfanoni, da bin ka’idoji da kuma haɓaka ƙungiyoyin masana’antu.

Waɗannan abubuwa, bisa ga rahoton na ERA 2023, ana bukatarsu a bangarori daban-daban ta fuskar ire-iren kamfanonin da ake da su da kuma ƙarfin fasaharsu.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

A nashi bangaren, Babban Jami’in Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Mista Matthias Schmale, wanda Masanin Tattalin Arziki, Nonso Obikili, ya wakilta, ya lura cewa abubuwa marasa dadi daban-daban, kamar illolin da annobar COVID-19 ta haifar, da yunkurin mamayar da Rasha ke yi a Ukraine, da sauyin yanayi sun sa Afirka ta fuskanci koma-baya wajen cimma muradun ci gaba mai dorewa na duniya (SDGs).

Ya ba da misali da yadda talauci a cikin 2021 ya karu sosai, lokacin da kusan ‘yan Afirka miliyan 30 suka fada kangin matsanancin talauci, inda hakan ya haifar da asarar ayyuka miliyan 22.

“Kasashe goma da suke da mafi yawan matalauta sun kai kashi 64.7% na nahiyar. Kasashe hudu na farko—Nijeriya (miliyan 100), Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo (miliyan 67), Tanzaniya (miliyan 36), da Habasha (miliyan 33)—sun dauki kashi 42% na talakawa da kef ama da talauci.” In ji Schmale.

Don haka, ERA 2023 ya yi kira da a samar da sabbin dabaru ga kasashen Afirka don magance kalubalen matsalar tattalin arzikin duniya. Rahoton ya yi kira da a inganta yadda ake magance matsaloli da samar da jajircewa ta hanyar tsare-tsare masu kyau na ci gaban kasa da shugabanci nagari, da kuma kawo sauyi ga tsarin ci gaban masana’antu.

Bugu da kari, mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki, Dokta Tope Fasua, ya bayyana koma-bayan tattalin arzikin da Nijeriya ta samu tun a shekarun baya da suka hada da: hauhuwar farashin kayayyaki a farkon shekarun 1970 bayan tashin gwauron zabon farashin mai a shekarar 1973; koma bayan shekarun 1980 saboda faduwar farashin kayayyaki; da kuma wani matsalar da aka samu a tsakiyar shekarun 2000 sakamakon faduwar danyen mai.

“Muna rayuwa cikin rashin daidaito ta fuskar tattalin arzikinmu, kuma yawancin Afirka har yanzu suna fama da irin wannan matsalar.” In ji shi.

Daga cikin wadanda suka halarci taron gabatar da rahoton akwai wakilan ofishin jakadancin Amurka, Tarayyar Turai, Sashen Bunkasa Ci Gaba na USAID, Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki ta Tarayya, Ma’aikatar Kudi, Babban Bankin Nijeriya da kuma hukumomin Majalisar Dinkin Duniya.

Wannan rahoto dai ya sake nuna yadda ake barin Nahiyar Afirka a baya ta fuskar hada-hadar kasuwanci a duniya duk da cewa akwai tarin albarkatun kasa da Allah ya huwace wa yankin inda ake danganta hakan da rashin samun shugabanci nagari a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023AfirkaAfricaEconomyRahotoTattalin ArzikiUN Report
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Taya Al-Sisi Murnar Lashe Zaben Shugabancin Masar

Next Post

‘Yan Fashin Daji Sun Halaka Mutum 1, Tare Da Sace Mutane 6 A Sokoto

Related

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

9 hours ago
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

3 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

4 weeks ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

'Yan Fashin Daji Sun Halaka Mutum 1, Tare Da Sace Mutane 6 A Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.