• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu

by Mairo Muhammad Mudi
8 months ago
in Labarai
0
Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani al’amari mai ban tsoro da ke faruwa a halin yanzu shi ne, yadda babu zato babu tsammani, ba kuma tare da wata alama ba; kwatam, sai ka ga maza sun fadi ringis; sun kasa mikewa.

A cikin shekarun baya-bayan nan, mun ga yadda wasu maza lafiyayyu; masu kuzari a jiki ke faduwa yayin gudanar da ayyukan motsa jiki. Wannan al’amari mai tayar da hankali, na ci gaba da yawaita a tsakanin al’umma tare da kawo mana bakin ciki a cikin rayuwarmu.

  • Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya
  • Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

Haka zalika, ba wai maza kadai ne irin wannan mutuwa ta fuju’an ke faruwa da su ba; har ma da matan, illa kawai dai na mazan ya fi rinjayar na mazan a zahiri.

A ‘yan shekarun nan, wani abin bakin ciki da takaici da har yanzu yana nan a raina shi ne, wani dan’uwan maigidana ne; wanda a zahiri mutum ne lafiyayye kuma dogo, dan wasan kwallon kwando, ya kasance kuma tauraro a kwallon kwandon; wanda yake wakiltar jiharmu da kuma kasa baki-daya.

Har ila yau, duk wanda ya kalle shi; zai ga lafiya ce ke tafiya karara tare da sha’awarsa; sakamakon ganin sa da ake yi yana motsa jiki a kowace yamma ta duniya, amma sai rashin sa’a ta taru da shi a ranar wata Alhamis, inda babu zato; babu tsammani ya yanke jiki ya fadi a filin wasa yana dauke da Azumi, tun daga nan bai sake motsawa ba; haka muka rasa shi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Haka nan, Dakta Mahmoud Muhammad; tsohon babban likitan asibitin IBB, sannan kuma tsohon babban sakatare a Jihar Neja, wanda shi ma tasa mutuwar ta yi matukar girgiza al’umma, wanda a cikin wani bidiyo mai tayar da hankali ya nuna shi cikin kuzari, yana buga kwallo a wani filin kwallo; kamar wani kwararren dan wasa, amma kafin kiftawar ido; ya fadi kasa, kamar wanda ya gaji yake son hutawa, sai kuma wannan ce kwanciyar tasa ta har abada.

Kazalika, shi ma wani sanannen matashi dan Kannywood; mai cike da kuzari, El-Muaz Muhammad; ya rasa rayuwarsa yayin da yake yin wannan wasa na kwallo, inda nan take ya fadi babu zato; babu tsammani, daga nan kuma sai ya ce ga garinku.

Irin wadannan abubuwan bakin ciki, na ci gaba da yawaita a takanin al’ummarmu. Wannan yasa nake tambayar abin da ke haddasa ire-iren wannan mutuwa ta fuji’an a tsakanin mazajenmu.

A matsayina na Musulma, na yarda da fadin Allah SWT cewa; “Kullu nafsin za’ikatul maut”, ma’ana; kowane mai rai zai dandani mutuwa, kuma babu wanda zai bar duniya kafin lokacinsa ya yi, amma duk da haka kuma, imaninmu ba zai taba cire mana alhakin kula da lafiyarmu ba.

Wadannan asarar rayukan da muke yi na mazajenmu, dole ne na yi kira da mu farka, musamman ma ga maza; wadanda galibi ke yin sakaci wajen kula da lafiyarsu, suna barin matansu na ci gaba da kasancewa a matsayin zawarawa; ‘ya’yansu kuma na zama marayu.

A al’ada, mun yarda da cewa; mutuwa ba ta da makawa, duk wanda lokacinsa ya yi; wajibi ne ya tafi. Sai dai abin mamaki kuma shi ne, yayin da muke kokarin jinkirta ko kauce mata, wasu daga cikin ayyukanmu na rashin sani; kan sanya mu matsa kusa da ita da gangan. Misali, muna kula da motocinmu da kyau kafin mu fara tafiya da su, haka nan ba za mu taba kwanciya a kan hanya ba, saboda zai kasance tamkar kisan kai ne.

Amma duk da haka, maza da yawa na yin sakaci da lafiyarsu, ba tare da suna kula da ita yadda ya kamata ba, suna kai kansu ga hadarin da ya kamata su rika gujewa.

A lokacin da nake aiki a ofishin jin kai na Asibitin Suleja, na lura da bambanci mai ban mamaki. Ofishinmu na kusa da dakin kula da masu ciwon hawan jini, a nan ne na fara lura cewa; galibin marasa lafiya mata ne. Wannan yasa na yi tunanin cewa, mata sun fi maza samun cutar hawan jinni; saboda damuwar da ke tattare da aure da rainon yara ga uwa.

Amma daga bisani, sai na gano cewa; yayin da mata ke zuwa neman magani idan ba su da lafiya ko suna dauke da juna biyu, maza kan yi shiru ne da bakinsu, ciwo na damunsu amma saboda kokarin nuna jarumta; sai su yi shiru har sai ya illata su.

Don haka, ya kamata maza su sani cewa; mu danginku muna bukatar ku cikin koshin lafiya, bai kamata ku rika sadaukar da rayuwarku; kuna matsa wa kanku wajen yin aiki tukuru ba, alhali jikinku yana son hutu.

Ku fara da yin gwaje-gwajen lafiyarku akai-akai a asibiti ko kuma a gida. Yanzu Bature ya kawo mana sauki, domin kuwa za ka iya sayen na’ura mai sarrafa kanta a cikin sauki wajen gwajin hawan jini da ciwon suga, sannan wannan na’ura za ta iya taimaka muku wajen samun bayanai ko shawarar ganin likita nan take; ko kuma batun daukar huta kafin ci gaba da motsa jikin da kuke yi na yau da gobe.

A nan, ba wai ina cewa wannan zai maye gurbin shawarar likita ba ne, amma zai iya zama tamkar wata fadakarwa ce mai matukar amfani; don neman taimakon gaggawa.

A takaice dai, ku kasance kuna cikin koshin lafiya; ku rika samun lokacin hutawa yadda ya kamata, sannan kuma ku tabbata kun kasance masu bayyana wa wadanda kuka yarda da su matsalolin da suke addabar ku.

Akwai alamomin da jikinku zai fada muku a daidai lokacin da kuke bukatar hutu; ku yi na’am da wannan sako, domin rayuwarku kyauta ce; lafiyarku kuma ba kawai taku ba ce, har ma da wadanda ke kaunarku.

Mazaje a manta da jarumtaka a bai wa jiki hakkinsa. Ku tabbata kuna hutawa a duk yayin da kuka gaji, idan jiki na yi muku ciwo; a yi maza a ga likita. Ba ma bukatar jarumtakarka, domin mun fi mukatarku da rai da kuma koshin lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Next Post

ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

Related

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

28 minutes ago
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
Labarai

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

4 hours ago
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa
Labarai

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

6 hours ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

7 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

8 hours ago
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn
Labarai

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

10 hours ago
Next Post
ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

ASUU Reshen Jami'ar Sa'adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.