• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Sarkin Kano Ya Roƙi ‘Yan Kasuwa Da Su Taimaka Su Rage Farashin Kayan Abinci

by Muhammad
2 years ago
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado-Bayero ya yi kira ga ‘yan kasuwa masu sayar da kayan masarufi da su rage tsadar kayan abinci da sauran kayayyaki domin bai wa talakawa damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.

Sarkin ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Zariya a lokacin bikin kaddamar da wani littafi mai suna: “Dauloli a Kasar Hausa” ma’ana ‘Masarautu a kasar Hausa’ na Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau.

Ado-Bayero ya kuma shawarci ’yan Nijeriya masu hannu da shuni da su rika taimakawa marasa galihu a lokacin azumin Ramadana.

Ya kuma yi addu’ar Allah Ta’ala ya kare rayukan al’umma su shaida wannan wata mai alfarma cikin koshin lafiya tare da yin addu’o’i a watan.

Sarkin ya yabawa mawallafin littafin, da ya yi bayani dalla-dalla kan masarautun Hausa a Kano da Katsina,l da Zamfara da Kebbi da Zazzau da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

“Bayanan da aka ba da cikakken bayani kan tsarin gudanar da mulki da kowace masarauta da sana’o’insu da ka’idoji da dabi’unsu,” inji shi.

Mai nazarin littafin, Farfesa Ahmed Zaria na Jami’ar Jihar Kaduna ya ce littafin mai shafi 356 yana da babi bakwai.

Ahmed Zaria ya ce littafin ya ba da cikakken labari da tarihin masarautun Hausa da siyasarsu da tsarin mulki da ka’idoji da dabi’u tun daga kafuwarsa zuwa yau.

Ya kara da cewa littafin ya zama dole kan dalibai ya kasance suna da kwafinsa da masu bincike a fannin ilimin harshe da tarihi.

Mawallafin littafin, Farfesa Gusau ya ce, littafin wani ƙoƙari ne na daidaita rubutaccen tarihin Masarautun Hausa inda ya ce galibin binciken da ake yi a jami’o’in kan masarautu kaɗan ne ba duka ba.

Gusau ya kara da cewa littafin kuma wani yunkuri ne na tallafawa juna da karfafa hadin kai a tsakanin masarautun Hausa da sauran ‘yan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
Manyan Labarai

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Next Post
Wasu Mazauna Abuja Sun Shiga Rumbun Ajiya Na Hukumar NEMA Sun Sace Kayan Abinci

‘Yansanda Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Sun Fasa Rumbun Ajiye Kayan Abinci A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.