• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Sarkin Kano Ya Roƙi ‘Yan Kasuwa Da Su Taimaka Su Rage Farashin Kayan Abinci

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado-Bayero ya yi kira ga ‘yan kasuwa masu sayar da kayan masarufi da su rage tsadar kayan abinci da sauran kayayyaki domin bai wa talakawa damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.

Sarkin ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Zariya a lokacin bikin kaddamar da wani littafi mai suna: “Dauloli a Kasar Hausa” ma’ana ‘Masarautu a kasar Hausa’ na Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau.

Ado-Bayero ya kuma shawarci ’yan Nijeriya masu hannu da shuni da su rika taimakawa marasa galihu a lokacin azumin Ramadana.

Ya kuma yi addu’ar Allah Ta’ala ya kare rayukan al’umma su shaida wannan wata mai alfarma cikin koshin lafiya tare da yin addu’o’i a watan.

Sarkin ya yabawa mawallafin littafin, da ya yi bayani dalla-dalla kan masarautun Hausa a Kano da Katsina,l da Zamfara da Kebbi da Zazzau da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

“Bayanan da aka ba da cikakken bayani kan tsarin gudanar da mulki da kowace masarauta da sana’o’insu da ka’idoji da dabi’unsu,” inji shi.

Mai nazarin littafin, Farfesa Ahmed Zaria na Jami’ar Jihar Kaduna ya ce littafin mai shafi 356 yana da babi bakwai.

Ahmed Zaria ya ce littafin ya ba da cikakken labari da tarihin masarautun Hausa da siyasarsu da tsarin mulki da ka’idoji da dabi’u tun daga kafuwarsa zuwa yau.

Ya kara da cewa littafin ya zama dole kan dalibai ya kasance suna da kwafinsa da masu bincike a fannin ilimin harshe da tarihi.

Mawallafin littafin, Farfesa Gusau ya ce, littafin wani ƙoƙari ne na daidaita rubutaccen tarihin Masarautun Hausa inda ya ce galibin binciken da ake yi a jami’o’in kan masarautu kaɗan ne ba duka ba.

Gusau ya kara da cewa littafin kuma wani yunkuri ne na tallafawa juna da karfafa hadin kai a tsakanin masarautun Hausa da sauran ‘yan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alh. Aminu Ado BayeroFarfesa Sa'idu Muhammad GusauGusaukanoKatsinaKebbiLittafin Dauloli a Kasar HausaRamadanSarkin KanoZamfaraZazzau
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Bada Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Sun Fasa Rumbun Ajiye Kayan Abinci A Abuja

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

27 minutes ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

5 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

9 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

10 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

1 day ago
Next Post
Wasu Mazauna Abuja Sun Shiga Rumbun Ajiya Na Hukumar NEMA Sun Sace Kayan Abinci

‘Yansanda Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Sun Fasa Rumbun Ajiye Kayan Abinci A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.