Ɗan wasan gaban Manchester United Marcus Rashford ya ce zai so ya taka leda tare da matashin ɗan wasa Lamine Yamal a Barcelona, Rashford mai shekaru 27, wanda ya shafe rabin kakar wasan bara ya na zaman aro a Aston Villa, a halin yanzu yana atisayen ƙara kuzari a ƙasar Sifaniya kafin a fara wasannin share fage na kulob ɗin, yayin da ake ta raɗe raɗin makomarsa a United.
Lokacin da aka tambaye shi game da yiwuwar yin wasa tare da Yamal, Rashford ya ce: “E, tabbas, kowa yana so ya yi wasa tare da mafi kyawun dan wasa, don haka nima inada wannan burin kuma zamu gani, Yamal, mai shekaru 17, ya taka rawar gani sosai yayin da Barcelona ta lashe kofuna uku a bana, kuma ta kai wasan kusa da na karshe a gasar zakarun Turai, hakazalika ya kuma taka rawar gani a nasarar da kasar Sifen ta samu a Euro 2024.
- Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?
- Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6
Rashford ya ƙara da cewa “Ba kowa ne zai iya yin abinda Yamal yayi a cikin shekaru 16-17 ba, don haka lallai akwai wata baiwa dangane da matashin ɗan wasan, Yana da matuƙar fikira idan ka kalli yadda yake sarrafa kwallo a kafarshi” Inji Rashford, rahotanni a watan Afrilu sun nuna cewa Rashford yana jin cewa da wuya ya sake bugawa Manchester United wasa a karkashin Ruben Amorim.
A watan Disamba ne dan ƙasar Portugal ɗin ya fitar da shi daga cikin tawagar United, kafin ya shafe sauran kakar a Aston Villa a matsayin aro, Daraktan wasanni na Barcelona Deco a baya ya ce kulob din yana son Rashford da Luis Diaz na Liverpool, sai dai duk da sha’awar da kulob din na Catalan ya nuna, kudi na iya zama cikas idan suka yi yunkurin siyan Rashford.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp