• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Dacewar Koya Wa ‘Ya’ya Taya Uwa Kishi

by Sister Iyami Jalo
2 years ago
in Zamantakewa
0
Rashin Dacewar Koya Wa ‘Ya’ya Taya Uwa Kishi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Iyaye mata kan rasa tunaninsu a yayin da bakin kishi ya lullbe mu su zuciya babu abin da su ke tunawa ban da duk wata hanyar da za su bi wajen cusgunawa amarya.

Dan haka yanzu nasihar Uwa ga yaranta ta tashi daga kan su yi ladabi da biyayya ga  na gaba da su, ta koma kan yadda za su yi rashin kunya da sharri da hada tuggu ga amarya don  kori ta.

  • Babu Wata Baraka Tsakanina Da Buhari – Tinubu
  • Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu

Wannan hali ya fi tasiri a kan ‘yaya mata fiye da ‘ya’ya  maza, wasu yaran maza su na daukar muguwar shawarar da uwa ta ke ba su a lokacin da su ke  da karancin shekarun amma da yawan yara maza idan sun fara girma ba su cika biyewa uwa ba, su kan ba ta shawara ma a kan ta daina damuwa.

Amma yara mata da ya ke a koda yaushe su na zaune ne a gida su na ara su yafa wajen taya mahaifiyarsu kishi har ma fi ta jin zafi da haushin amaryar.

Sai Uwa ta koma gefe ta na jin dadi ta na cewa ba da ni za ta yi kishi ba na bar ta da yara.

Labarai Masu Nasaba

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

Amarya ta na shiga tashin hankali da rashin sukuni da zarar an ce maigida zai fita sai gabanta ya yi ta faduwa don zai tafi ya bar ta da yaran gidan, don ba za su iya yi mata komai a gabansa ba saboda su na tsoro kuma ba za su bari ya ga wata alama ba a gabansa don haka ko amarya ta kai kara su na da yawa su na da bakin da za su zakalkale su juya mata magana, yau da gobe har uba ya fara zargin amarya da tsanar ‘yayansa da matarsa ta fari.

Karshe dai idan amarya ta ji wuya sai ta fita ta bar musu gidan ta bar kananan yaranta su hadu su wahalar da su, sai ta koma gidansu ta yi ta fama da zawarci. Burin uwa da yaranta ya cika an tafi an bar musu gidan su kadai.

Ka da mu manta komai nisan jifa kasa zai fado, haka duk abin da ka cuka shi za ka girba, tabbas bahaushe ya yi gaskiya haka batun ya ke. Idan amarya ta yi hakuri yau da gobe ta na zamanta abin da uwarsu ta koya mu su zai koma kanta domin idan ta na sawa su yiwa amaryarta rashin kunya gobe ita  za su yiwa. Ba ta isa ta hana su ba kuma ba ta da bakin da za ta yi mu su tsawa domin ita da bakinta ta ce su je su zagi babba koma su bangaje matar uba, matar uba kuwa  ai uwa ce a gare su.

Dan haka ka da uwa ta yi mamaki idan yaranta su ka fara yi mata mu su su na yi mata rashin kunya, ta saka su aiki su ki yi, ta dake su su na kokarin ramawa ta zage su su na cewa ba dai nawa ba. Kuma duk yadda za su kai ga lalacewa babu abin da ya shafi uba ke uwa ke ce a ciki tsundum ko da uba ya na jin ciwon abin da su ke yi a ransa ke uwa sai kin fi jin zafi tunda ke ce ki ke yini da kwana tare da su a gida daya kuma a daki daya.

Ba za ki san kin tafka kuskure ba sai sanda ki ka yi musu aure musamman su ka je su ma su ka iske wasu matan a gidan, matan kuma su na da yara, abin da ka cuka fa shi za ka girba, sakayyar Allah kuwa tun daga duniya a ke tsinta, ‘ya’yan miji fa za su takurawa yaranki abin da ba su yi ba ma za’a yi musu, ko wahala da bakin ciki bai sa sun fito ba tabbas za su yi zaman wahala da takaici ba komai ba ne illa hakkin amaryar Mahaifinsu da ya ke bibiyarsu.

Yadda a gidansu su ka gani mahaifiyarsu ba ta mutunta a abokiyar zamanta ta dauke ta abokiyar gabarta duk da biyayyar da amaryar ta ke yi mata a banza, su ma yara sun saka hakan a cikin zuciyarsu dan haka idan su ka tarar da wata a gidan tabbas abokiyar gaba za su dauke ta ayi ta fada, haka kuma idan aka auro mu su  wata daga baya ba za su yarda a zauna lafiya ba, kin ga kenan kin bata tarbiyar zuri’arki gaba daya su ma ‘yayansu haka za su tashi su koyawa ‘ya’yansu haka haka za’ayi ta tafiya har danginku ya sami mummunar shaida a ce kada a auri ire-irenku ma su dukan kishiya ko danbe da kishiya.

Ki sa ni ko ki na raye ko ba kya raye ki na da kwamishon alhaki a dukka rashin tarbiyyar da ya ke faruwa da zalumci da ‘yayanki da jikokinki su ke yi. Ki tuna akwai mutuwa akwai rashin lafiya wannan amarya ita za ta rike yaranki watarana idan ba kya nan, dan haka ki nunawa yaranki ita ma uwarsu ce dole su girmama ta kamar yadda za su girmamaki da mahaifinsu. Idan ki ka yi haka sai kin fi kowa cin ribar abin nan gaba.

Mun samo muku daga kundin ajiyarmu, kamar yadda JAMILA UMAR TANKO (JUT) ta taba rubuto mana


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Ya'YaKishiUwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu

Next Post

Ra’ayoyinku  A Kan Yarfen Da ‘Yan Takarar Shugabancin Kasa  Ke Yi Wa Junansu

Related

‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
Taskira

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

2 months ago
Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
Taskira

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

2 months ago
Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?
Taskira

Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?

3 months ago
Maganin Zubewar Mama Da Yadda Ake Gyara Shi 
Taskira

Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida

5 months ago
Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?
Taskira

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

8 months ago
Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?
Taskira

Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?

1 year ago
Next Post
Ra’ayoyinku  A Kan Yarfen Da ‘Yan Takarar Shugabancin Kasa  Ke Yi Wa Junansu

Ra’ayoyinku  A Kan Yarfen Da ‘Yan Takarar Shugabancin Kasa  Ke Yi Wa Junansu

LABARAI MASU NASABA

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.