• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Kasuwa Da Cin Zarafi Na Cikin Manyan Kalubalen Kannywood – Sani Abubakar

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Nishadi
0
Rashin Kasuwa Da Cin Zarafi Na Cikin Manyan Kalubalen Kannywood – Sani Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Wannan ita ce karshen tattaunawa da Jarumi SANI ABUBAKAR da muka fara kawowa a makon da ya gabata tare da wakiliyarmu, RABI’AT SIDI BALA. A karanta har karshe don jin abubuwan ta kunsa kamar haka:

Tun daga farkon farawarka kawo yanzu wanne irin kalubale ka fuskanta cikin masana’antar?

Shi kalubale ba a rasa shi, a gaskiyar magana tun daga farko kawo yanzu ba zan iya cewa ga wani babban kalubale dana hadu da shi ba face rashin kasuwa, yadda sana’ar ta canja ba yadda take da farko ba akalarta ta juya ta yi canji kala-kala, wannan canji da ta kawo bangaren kasuwa shi ne kawai kalubalen. Sannan babban abin da ya fi damu na shi ne za ka ga mutum ya fito ya ci zarafinmu amma ba mu da ikon ramawa su ma shuwagabanninmu sai dai kawai su zuba ido saboda gudun kar mutum ya zo yayi magana wani ya fadi maganar da hankalinka ba zai iya dauka ba, gaskiya wadannan shi ne matsalolin da nake ganin su ka fi damuna. za ka ga mutumin da bai ma san ya sana’ar taka take ba, bai ma taba zuwa ya ga ya ma ake sana’ar ba, bai san ya aka fara ta ya ake kare ta ba, amma za ka ga ya fito yana cin mutunci, ko cin zarafi yana zaginku a cikin masana’antar, kuma karshe dai abu daya kawai za a yi a ce a yi hakuri. Babu wata masana’anta ko wajen sana’a da za ka tarar ana zagin mutum ko ana cin zarafinsa kuma babu yadda zai yi sai masana’antar Kannywood. Ni dai tunda nake cikin masana’antar babu wani wanda ya taba daukar wani tallafi ya ce ga wani tallafi an ba da domin ci gaban masana’antar in dai ba maigidana ba, na tabbatar sanata ya taimaki ‘yan kannywood wanda kuma duk abin da aka yi kusan da hannuna ma a ciki, amma kalubale na cin mutunci da cin zarafi dai muna gani.

Ba ka ganin wasun cikinku ne ke nemo muku zagin, ta yadda suke tafiyar da nasu al’amuran har ta kai da an yi muku kudin goro, ko ya abun yake?

Gaskiyar magana guda daya ita ce; duk cikin al’ummar da ki ka gani, kuma kowacce irin masana’anta a duniya dole akwai bata gari a cikinta kuma akwai na kirki, dan haka babu yadda za a ce mu wankakku ne dan muna wannan maganar, a’a! dole akwai bata gari a cikinmu. Amma maganar na ce wani ne yake janyo mana zagi a’a! ai bai kamata ka yi shari’a ba tare da, ka san me ye yake faruwa ba. Dole a cikin al’umma idan kana sana’a sai ka tarar da bata gari da zai ja maka zagi wannan kuwa mun sani, hatta a cikinku ‘yan jarida ku kun sani akwai wadanda bata gari ne suke ja muku zagi akan sana’arku, ba za ku ce ku a cikin sana’arku babu mai zaginku ba, a kowacce sana’a ana zagin mutane.

Na ji ka ce ba wanda ya taba ba ka wani tallafi a masana’antar, to ya batun kallon da sauran jama’a ke yi wa ‘yan kannywood na cewar; suna tafiya ne da gwamnati, yayin da jam’iyya tayi nasara tana ware musu wasu kudade na daban, me za ka ce akan hakan?

Gaskiyar magana shi dan fim zai iya yin siyasa, misali; kamar ni kin ga tunda nake da maigidana  nake tafiya tare da shi, ni ba jam’iyya nake bi ba, bayan zaben maigidana zan duba na ga wa ya cancanta na zabe shi?, kuma ni bana bin wani dan siyasa bayan maigidana, akwai masu yin hakan amma akwai wanda ba sa canja jam’iyya a ‘yan kannywood din. Kuma dole ai dan fim yayi siyasa saboda siyasa ta kowa ce dole ka duba ka ga ya za a yi al’ummarka ta zama gyararriyar al’umma?, misali; dole ka  duba ka hanga ka gani wane ne zai taimaki al’umma, inda gudunmawar da za ka ba shi kai ma ka bada taka irin gudunmawar, ni kin ga Barau Jibril Maliya ne maigidana, dan haka dole ina bin sa dan na tabbatar da cewa inada yakini dari bisa dari yana kyautatawa al’umma.

Ya batun nasarori fa, wanne irin nasarori ka samu game da fim?

Sai dai na ce Alhamdulillahi dan ban isa ma na ce ga iyakacinsu ba, an same su da yawa burjik kuma ana kan samu, dan cikin sana’ar Allah ya rufa ma asiri ai ka gama samun nasara, an samu nasarori babu iyaka gaskiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farashin Shinkafa Zai Ƙaru Da Kashi 40%, Masara Da Kashi 25% A Shekarar 2024 – AFEX

Next Post

Zan Bar Barcelona A Karshen Kakar Wasanni Ta Bana-Xavi

Related

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

3 days ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

2 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

3 weeks ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

3 weeks ago
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

1 month ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 month ago
Next Post
Zan Bar Barcelona A Karshen Kakar Wasanni Ta Bana-Xavi

Zan Bar Barcelona A Karshen Kakar Wasanni Ta Bana-Xavi

LABARAI MASU NASABA

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.