• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Katabus Da Nijeriya Ta Yi A Gasar Olympics

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
9 months ago
in Wasanni
0
Rashin Katabus Da Nijeriya Ta Yi A Gasar Olympics
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta sake tafka irin abin kunyar da ta yi a London, shekaru 12 da suka wuce, bayan da ta sake yin abin junya a gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya, wato Olympic, inda ‘yan wasan Nijeriya 88 da suka wakilci kasar nan suka dawo ba tare da cin kyauta ko guda daya ba.

 

A cikin ‘yan wasa 88 da suka tafi Birnin Paris din kasar Faransa domin wakiltar Nijeriya a wasannin, babu dan wasa ko guda daya da ya yi kokarin lashe sarkar gwal, duk da kirarin da ake yi wa Nijeriya na cewa ita ce uwa maba da mama.

  • Saka Ya Saka Murmushi A Fuskar Magoya Bayan Arsenal
  • Sin Ta Samu Ci Gaba A Fannin Raya Jarin Fasahohin Kere-Kere Da Kaso 10.9% A Watanni 7 Na Farkon Bana

Tuni dai Ministan Wasanni, John Enoh, ya bayyana rashin kokarin a matsayin abin kunya, domin ‘yan wasan kwallon kwando na D’Tigress ne kadai suka samu nasarar lashe wasanni biyu na cikin rukuni, inda suka doke kasashen Australia da Canada, kuma ‘yan wasan sun kafa tarihin kasancewa kasar Afirka ta farko da ta samu zuwa matakin wasan kusa da na kusa da na karshe a wasannin kwallon kwandon.

 

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Tawagar mata ta kwallon kafa ma dai tun a cikin rukuni aka yi waje da ita, sannan ‘yan wasan da suka wakilci kasar nan a wasannin kokawa da wasannin kokawa da wasan daga nauyi da wasan kwallon tabir duka an fitar da su ne da wuri daga gasar.

 

Sai dai daman tun daga gasar da aka buga a Birnin London shekaru 12 da suka gabata, Nijeriya ta samu nasarar lashe sarka guda uku ne kawai cikin shekaru 12, inda a shekarar 2016 a Birnin Rio na Brazil ‘yan wasan kwallon ‘yan kasa da shekara 23 suka samu tagulla, sai a birnin Tokyo na Japan ‘yar wasan kokawa Blessing Oborodudu ta samu tagulla itama, sai Ese Brume wadda ta samu tagulla itama a Japan din.

 

Amma akwai kasashen Afirka da suka fi Nijeriya tabuka abin arziki musamman kasar Botswana da ta lashe sarkar gwal ta gudun mita 200, wadda kuma hakan ya kasance kasar Afirka ta farko da ta taba lashe wannan kyauta, sai Kenya wadda ta lashe gwal guda hudu sai Algeriya mai guda biyu, sai kasashen Uganda da Tunisia da Afirka ta Kudu da Ethiopia da Masar da kuma Morocco duka sun samu gwal guda dai-dai.

 

Sai dai akwai ‘yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwal amma sun wakilci wasu kasashen daban, ‘yan wasan sun hada da Salwer Eid Naser, da Samuel Omorodion da Yemisi Ogunleye da kuma Annette Echikunweke duka sun wakilci kasashe daban-daban kuma sun lashe sarkoki.

 

Amma wasu suna ganin akwai bukatar gwamnati ta dauki mataki a nan gaba ta hanyar farfado da wasanni tun daga makarantun firamare zuwa makarantun gaba da sakandire da kuma dawo da wasanni a unguwanni domin karfafawa matasa gwiwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ta’addanci: Burkina Faso Na Neman Karin Mayakan Sa-kai

Next Post

Sojoji Sun Kashe Wasu ‘Yan Bindiga A Zamfara

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

1 day ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

1 day ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

4 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

4 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

5 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

6 days ago
Next Post
Sojoji

Sojoji Sun Kashe Wasu ‘Yan Bindiga A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.