ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Katabus Da Nijeriya Ta Yi A Gasar Olympics

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Olympics

Nijeriya ta sake tafka irin abin kunyar da ta yi a London, shekaru 12 da suka wuce, bayan da ta sake yin abin junya a gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya, wato Olympic, inda ‘yan wasan Nijeriya 88 da suka wakilci kasar nan suka dawo ba tare da cin kyauta ko guda daya ba.

 

A cikin ‘yan wasa 88 da suka tafi Birnin Paris din kasar Faransa domin wakiltar Nijeriya a wasannin, babu dan wasa ko guda daya da ya yi kokarin lashe sarkar gwal, duk da kirarin da ake yi wa Nijeriya na cewa ita ce uwa maba da mama.

ADVERTISEMENT
  • Saka Ya Saka Murmushi A Fuskar Magoya Bayan Arsenal
  • Sin Ta Samu Ci Gaba A Fannin Raya Jarin Fasahohin Kere-Kere Da Kaso 10.9% A Watanni 7 Na Farkon Bana

Tuni dai Ministan Wasanni, John Enoh, ya bayyana rashin kokarin a matsayin abin kunya, domin ‘yan wasan kwallon kwando na D’Tigress ne kadai suka samu nasarar lashe wasanni biyu na cikin rukuni, inda suka doke kasashen Australia da Canada, kuma ‘yan wasan sun kafa tarihin kasancewa kasar Afirka ta farko da ta samu zuwa matakin wasan kusa da na kusa da na karshe a wasannin kwallon kwandon.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Tawagar mata ta kwallon kafa ma dai tun a cikin rukuni aka yi waje da ita, sannan ‘yan wasan da suka wakilci kasar nan a wasannin kokawa da wasannin kokawa da wasan daga nauyi da wasan kwallon tabir duka an fitar da su ne da wuri daga gasar.

 

Sai dai daman tun daga gasar da aka buga a Birnin London shekaru 12 da suka gabata, Nijeriya ta samu nasarar lashe sarka guda uku ne kawai cikin shekaru 12, inda a shekarar 2016 a Birnin Rio na Brazil ‘yan wasan kwallon ‘yan kasa da shekara 23 suka samu tagulla, sai a birnin Tokyo na Japan ‘yar wasan kokawa Blessing Oborodudu ta samu tagulla itama, sai Ese Brume wadda ta samu tagulla itama a Japan din.

 

Amma akwai kasashen Afirka da suka fi Nijeriya tabuka abin arziki musamman kasar Botswana da ta lashe sarkar gwal ta gudun mita 200, wadda kuma hakan ya kasance kasar Afirka ta farko da ta taba lashe wannan kyauta, sai Kenya wadda ta lashe gwal guda hudu sai Algeriya mai guda biyu, sai kasashen Uganda da Tunisia da Afirka ta Kudu da Ethiopia da Masar da kuma Morocco duka sun samu gwal guda dai-dai.

 

Sai dai akwai ‘yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwal amma sun wakilci wasu kasashen daban, ‘yan wasan sun hada da Salwer Eid Naser, da Samuel Omorodion da Yemisi Ogunleye da kuma Annette Echikunweke duka sun wakilci kasashe daban-daban kuma sun lashe sarkoki.

 

Amma wasu suna ganin akwai bukatar gwamnati ta dauki mataki a nan gaba ta hanyar farfado da wasanni tun daga makarantun firamare zuwa makarantun gaba da sakandire da kuma dawo da wasanni a unguwanni domin karfafawa matasa gwiwa.

Olympics
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Olympics
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Sojoji

Sojoji Sun Kashe Wasu ‘Yan Bindiga A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.