ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Katabus Da Nijeriya Ta Yi A Gasar Olympics

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Olympics

Nijeriya ta sake tafka irin abin kunyar da ta yi a London, shekaru 12 da suka wuce, bayan da ta sake yin abin junya a gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya, wato Olympic, inda ‘yan wasan Nijeriya 88 da suka wakilci kasar nan suka dawo ba tare da cin kyauta ko guda daya ba.

 

A cikin ‘yan wasa 88 da suka tafi Birnin Paris din kasar Faransa domin wakiltar Nijeriya a wasannin, babu dan wasa ko guda daya da ya yi kokarin lashe sarkar gwal, duk da kirarin da ake yi wa Nijeriya na cewa ita ce uwa maba da mama.

ADVERTISEMENT
  • Saka Ya Saka Murmushi A Fuskar Magoya Bayan Arsenal
  • Sin Ta Samu Ci Gaba A Fannin Raya Jarin Fasahohin Kere-Kere Da Kaso 10.9% A Watanni 7 Na Farkon Bana

Tuni dai Ministan Wasanni, John Enoh, ya bayyana rashin kokarin a matsayin abin kunya, domin ‘yan wasan kwallon kwando na D’Tigress ne kadai suka samu nasarar lashe wasanni biyu na cikin rukuni, inda suka doke kasashen Australia da Canada, kuma ‘yan wasan sun kafa tarihin kasancewa kasar Afirka ta farko da ta samu zuwa matakin wasan kusa da na kusa da na karshe a wasannin kwallon kwandon.

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Tawagar mata ta kwallon kafa ma dai tun a cikin rukuni aka yi waje da ita, sannan ‘yan wasan da suka wakilci kasar nan a wasannin kokawa da wasannin kokawa da wasan daga nauyi da wasan kwallon tabir duka an fitar da su ne da wuri daga gasar.

 

Sai dai daman tun daga gasar da aka buga a Birnin London shekaru 12 da suka gabata, Nijeriya ta samu nasarar lashe sarka guda uku ne kawai cikin shekaru 12, inda a shekarar 2016 a Birnin Rio na Brazil ‘yan wasan kwallon ‘yan kasa da shekara 23 suka samu tagulla, sai a birnin Tokyo na Japan ‘yar wasan kokawa Blessing Oborodudu ta samu tagulla itama, sai Ese Brume wadda ta samu tagulla itama a Japan din.

 

Amma akwai kasashen Afirka da suka fi Nijeriya tabuka abin arziki musamman kasar Botswana da ta lashe sarkar gwal ta gudun mita 200, wadda kuma hakan ya kasance kasar Afirka ta farko da ta taba lashe wannan kyauta, sai Kenya wadda ta lashe gwal guda hudu sai Algeriya mai guda biyu, sai kasashen Uganda da Tunisia da Afirka ta Kudu da Ethiopia da Masar da kuma Morocco duka sun samu gwal guda dai-dai.

 

Sai dai akwai ‘yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwal amma sun wakilci wasu kasashen daban, ‘yan wasan sun hada da Salwer Eid Naser, da Samuel Omorodion da Yemisi Ogunleye da kuma Annette Echikunweke duka sun wakilci kasashe daban-daban kuma sun lashe sarkoki.

 

Amma wasu suna ganin akwai bukatar gwamnati ta dauki mataki a nan gaba ta hanyar farfado da wasanni tun daga makarantun firamare zuwa makarantun gaba da sakandire da kuma dawo da wasanni a unguwanni domin karfafawa matasa gwiwa.

Olympics
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
Olympics
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Sojoji

Sojoji Sun Kashe Wasu ‘Yan Bindiga A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.