ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Katabus Da Nijeriya Ta Yi A Gasar Olympics

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Olympics

Nijeriya ta sake tafka irin abin kunyar da ta yi a London, shekaru 12 da suka wuce, bayan da ta sake yin abin junya a gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya, wato Olympic, inda ‘yan wasan Nijeriya 88 da suka wakilci kasar nan suka dawo ba tare da cin kyauta ko guda daya ba.

 

A cikin ‘yan wasa 88 da suka tafi Birnin Paris din kasar Faransa domin wakiltar Nijeriya a wasannin, babu dan wasa ko guda daya da ya yi kokarin lashe sarkar gwal, duk da kirarin da ake yi wa Nijeriya na cewa ita ce uwa maba da mama.

ADVERTISEMENT
  • Saka Ya Saka Murmushi A Fuskar Magoya Bayan Arsenal
  • Sin Ta Samu Ci Gaba A Fannin Raya Jarin Fasahohin Kere-Kere Da Kaso 10.9% A Watanni 7 Na Farkon Bana

Tuni dai Ministan Wasanni, John Enoh, ya bayyana rashin kokarin a matsayin abin kunya, domin ‘yan wasan kwallon kwando na D’Tigress ne kadai suka samu nasarar lashe wasanni biyu na cikin rukuni, inda suka doke kasashen Australia da Canada, kuma ‘yan wasan sun kafa tarihin kasancewa kasar Afirka ta farko da ta samu zuwa matakin wasan kusa da na kusa da na karshe a wasannin kwallon kwandon.

 

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Tawagar mata ta kwallon kafa ma dai tun a cikin rukuni aka yi waje da ita, sannan ‘yan wasan da suka wakilci kasar nan a wasannin kokawa da wasannin kokawa da wasan daga nauyi da wasan kwallon tabir duka an fitar da su ne da wuri daga gasar.

 

Sai dai daman tun daga gasar da aka buga a Birnin London shekaru 12 da suka gabata, Nijeriya ta samu nasarar lashe sarka guda uku ne kawai cikin shekaru 12, inda a shekarar 2016 a Birnin Rio na Brazil ‘yan wasan kwallon ‘yan kasa da shekara 23 suka samu tagulla, sai a birnin Tokyo na Japan ‘yar wasan kokawa Blessing Oborodudu ta samu tagulla itama, sai Ese Brume wadda ta samu tagulla itama a Japan din.

 

Amma akwai kasashen Afirka da suka fi Nijeriya tabuka abin arziki musamman kasar Botswana da ta lashe sarkar gwal ta gudun mita 200, wadda kuma hakan ya kasance kasar Afirka ta farko da ta taba lashe wannan kyauta, sai Kenya wadda ta lashe gwal guda hudu sai Algeriya mai guda biyu, sai kasashen Uganda da Tunisia da Afirka ta Kudu da Ethiopia da Masar da kuma Morocco duka sun samu gwal guda dai-dai.

 

Sai dai akwai ‘yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwal amma sun wakilci wasu kasashen daban, ‘yan wasan sun hada da Salwer Eid Naser, da Samuel Omorodion da Yemisi Ogunleye da kuma Annette Echikunweke duka sun wakilci kasashe daban-daban kuma sun lashe sarkoki.

 

Amma wasu suna ganin akwai bukatar gwamnati ta dauki mataki a nan gaba ta hanyar farfado da wasanni tun daga makarantun firamare zuwa makarantun gaba da sakandire da kuma dawo da wasanni a unguwanni domin karfafawa matasa gwiwa.

Olympics
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Olympics
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Sojoji

Sojoji Sun Kashe Wasu ‘Yan Bindiga A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.