ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Shugabaci Nagari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki, In Ji SDP

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
SDP

Jam’iyyar SDP reshen jihar Katsina ta bayyana cewa halin kunci da ‘yan ƙasar ke ciki yana da alaƙa ta kusa da kusa da rashin shuwagabanni masu nagarta waɗanda suke kishin talakawa.

Shugaban jam’iyyar SDP a jihar Katsina Alhaji Bello Safana ya bayyana haka a lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Katsina

Alhaji Bello Safana ya koka akan halin rashin tsaro da ya sanyo Katsina gaba inda ya ce kullum sai an kawo hari yanzu abin har cikin kwaryar Katsina.

ADVERTISEMENT
  • Gwamna Wike Ya Karyata Batun Maka Atiku Da Tambuwal A Kotu

 

Haka kuma jam’iyyar ta SDP a matakin jihar Katsina sun bayyana cewa, sun fito ne domin kwatowa al’umma haƙƙinsu da ceto talakawa daga halin da suke ciki musamman matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Tunda farko Alhaji Bello Safana ya fara ne da bada tarihin yadda wannan tafiya ta su ta faro daga wani dandali da masu rajin kawo gyara a cikin al’umma.

Ya ce wannan tafiya Alhaji Usman Bujaje ne ya assasa ta domin a ɗora wani harsashi samar da yanayin da zai bada damar samun shuwagabannin na gari da za su jagoranci al’umma da adalci anan gaba.

Shugaban jam’iyyar SDP ya ce sun yi zaɓen shugabanni sannan sun samar da ‘
‘yan takarkari a matakin gwamna wanda Ibrahim Zakari shine ɗan takarar su na gwamnan Katsina sannan suna da
‘yan takarar majalisar dokokin jiha 18 dakuma na majalisar tarayya.

Sannan a madadin ita kanta jami’yyar SDP da magoya bayan ta a fadin jihar Katsina suna jajanta wa al’umma bisa hali na rashin tsaro da aka shiga cikin sa, kuma suna fatan cewa idan aka zaɓe su za su kawo canji mai ma’ana.

Shima a nashi jawabin sakataren jam’iyar SDP na jihar Katsina Alhaji Mustapha Kurfi ya nuna halin damuwa akan yadda jama’a suka shiga halin rashin tabbas da rashin sanin makomar ƙasa baƙi ɗaya

Haka kuma shuwagabannin jam’iyyar SDP sun nuna rashin gamsuwa da yadda ake da tafiyar da sha’anin tsaro a Najeriya da kuma jihar Katsina wanda suke ce ta hanyar shuwagabannin na gari ne kawai za a yi Kawo karshen wannan matsala

 

  • https://leadership.ng/gods-plan-for-nigeria-will-manifest-says-sdp-presidential-candidate/

Daga karshe shuwagabannin jam’iyyar SDP sun bayyana cewa an shirya tsaf domin tunkarar duk wani ƙalubale na siyasa ta hanyar sanar da al’umma hali da jihar Katsina da kuma ƙasa baki ɗaya suke ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Next Post
Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.