• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

by Idris Aliyu Daudawa
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Azuzuwan makarantu a Jihohin Benuwe, Katsina da kuma Neja yanzu an maida su wuraren kwana na muatne ƴan gudun Hijira waɗanda aka raba su da gidajensu sanadiyar ayyukan ta’addancin da ƴan ta’adda suke yi. Dubban yaran da suke waɗanɗan Jihohin yanzu basu zuwa makarantu saboda kuwa makarantun nasu an maida su, matsugunnin mutane ƴan gudun hijira.

Halin da ake ciki kuma yanzu basu san ranar da za su koma makaranta ba, irin hakan ta sa ake ganin ko shakka babu lamarin karatu zai haɗu matsala a wuraren kamar yadda rahotannin jaridar, Trust ta ƙarshen suka nuna.

A Jihar Benuwe, babu wanda zai iya faɗar yadda za’a yi da irin yadda yaran da suka isa shiga makaranta, waɗanda matsalar ƴan ta’adda ta lalata wurarensu, waɗanda kuma mutanen ne suka mamaye makaratun domin su samarwa kansu wuraren da za su riƙa kwana.

  • Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar
  • SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

Rahotanni sun nuna muatane da yawa daga rikicin ta’addanci ya fi shafar ƙananan hukumomi sun haɗa da Guma, Logo, Agatu, Kwande, Gwer ta Yamma, Apa da kuma Makurdi, yanzu al’ummar ƙananan hukumomin suna kwana ne a makarantu, hakan kuma ya kawo tsayawar harkokin da suka shafi karatu.

Wata mahaifiya, Anita Ikyur, ta ce makaranta Firamare ta NKST, a ƙaramar hukumar Logo da daɗewa ne ta zama mazauni shekarar biyar.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Wani mahaifi, Mande Achagh, ya ce matsalar ta fi yin ƙamari a gundumarsa ta Agagbe, a ƙaramar hukumar Gwer West inda yawancin waɗanda basu da matsuguni suka samu mafaka, a wurare na musamman, makarantu, da kuma wasu gundumomi na al’umma.

“Matsalar tafi matuƙar lalacewa a Gwer ta Yamma abin kuma ya shafi makarantu sosai. Ina fatan gwamnati zata kalli lamarin domin ta ɗauki mataki, wajen samarwa mawaɗanda suka rasa matsuguni wuraren zama ta haka ‘ya’yanmu za su iya koma harkar karatu ta amfani da azuzuwansu.

“Irin matsalar da su yaran namu suke fuskanta dangane da karatunsu ba abinda za ayi wa riƙon sakainar kashi bane. Abin yana matauƙara ɓata mani rai, saboda wasu wuraren yara suna karatu ne a ƙarƙashin itatuwa, yayin da wasu kum asuka daina zuwa makaranta gaba ɗaya kamar yadda Achagh ya ce”.

Ga Jacintha Terhemen, wadda ita ɗalibi ce ‘yar makarantar Sakandare a wani harin ta’addanci da aka kai a Yelwata, ƙarƙashin ƙaramar hukumar Guma, cewa tayi duk da yake, makarantar da take abin bai shafe ta,ba saboda babu mutanen da suke kwana, amma, a, makarantun Firamare ana amfani ne, da su tare da mutanen da ta’addancin ƴan ta’adda ya raba su da garuruwan su.

“A sansanonin Ugba a Logo da Ortese a Guma, ana zuwa makaranta yayin da suma ƴan gudun Hijirar suna nan. Gwamnatin Jihar Benuwe ta ƙaddamar da wani tsari na samar da wuraren kwana masu inganci, amma hanya da za abi ita ce take da wahala sai an sa haƙuri.

An riga an sa tsari, gwamnati kuma tana neman taimako daga majalisar ɗinkin duniya da kuma Tarayyar Turai da sauran abokan tafiya masu taimakawa daga waje domin a aiwatar da shi tsarin. Aikin ana sa ran zai ci Naira Tiriliyan ɗaya, don haka abin yana buƙatar kuɗi da yawa ya kuma ƙunshi dukkan abubuwan more rayuwa waɗanda daga ƙarshe za su kawo ƙarshen matsalolin da ake fuskanta.

Neja

Makarantun da ake amfani da su a Jihar Neja wajen matsugunnin ƴan gudun Hijira sun haɗa da Central Firmare, Gwada; Central Firamare School, Kuta and Central Firamare, Erena, dukkansu a ƙaramar hukumar Shiroro.

Ɗaya daga mutanen da suka rasa matsuguni, Ahmed Almustapha, da yake sansanin Kuta, ya shaidawa Jaridar ƙarshen mako cewa wasu daga cikin yaran an maida su zuwa Model Firamare yayin da ƴan azuzuwa ne aka bar ma, sha’anin da ya shafi karatu a Central Firamare.

“Ba duka azuzuwa bane, ƴan gudun hijirar suke amfani da su ba. Wasu azuzuwan har yanzu ana amfani da su ne wajen yin karatun yara a makaranta, amma wasu Iyaye sun cire ‘ya’ansu daga Central Firamare,wurin da, ƴan gudun hijira suke zama, suka sasu a makarantar Model, Firamare.’Ya’yan mutanen da ta’addanci ya rutsa da sune kawai basu zuwa makaranta yanzu.

Wasu malaman da suke koyarwa ƴan sa kai su kan zo su koyar da su, amma yanzu sun bar zuwa.Bamu san dalilin da yasa ba,”.

Da yake makarantun da abin ya shfa ƴan gudun Hijira ne suke kwana, yawancin ƴan makarantar, an tilasta masu ne su koma wata makarantar, ko gaba ɗaya ma su bar zuwan. Wannan halin ba wai lamarin karatu kaɗai ya shafa ba,ƴan makaranta da Malamai, har ma ya maida wasu abubuwan da ake amfani, da su, sun lalace, hakan yasa cikin makarantar bai da wata sha’awar kallo . Shugaban makarantar Central Firamare, Kuta, Ya’u Ibrahim ya ce an bar shi da azuzuwa 9 kaɗai bayan kuma ga yawan ƴan makaranta da ya kai 1,360, inda yace sauran azuzuwan ƴan gudun hijira ne suke zama.

Tsaro

Ibrahim ya nuna rashin jin daɗinsa akan irin halayen su ƴan gudub hijirar, musamman ma yadda suke yin kashi a fili wanda yin hakan ba ƙaramar matsalar da take shafar lafiya bace, ga su Malamai, da kuma ƴan makaranta.

“Maganar gaskiya kasancewar ’yan gudun hijira ba ƙaramar matsala bace ga lamarin daya shafi lafiya gare mu. Suna kashi duk inda suka ga dama cikin makaranta, yanzu ko ina wari yaje yi.

“Yaran da su ma basu da matsuguni ba a sa su, makaranta ta, ba; ban san ko wane dalili bane ya sa. Babu waniɗan makarantarmu da ya bari saboda akwai ƴan gudun hijira a makarantarmu. Babbar matsalar da muke fuskanta ita ce rashin isassun azuzuwa saboda sai da muka raba ƴan makarantar uku, wato kowace rana da akwai waɗanda za su zo saboda yawansu ana kuma son a kauce ma cunkoso. Ga kuma irin yadda ake zama a sansanin wani abin damuwa ne shi ma kamar yadda ya ƙara jaddadawa”.

Katsina

An lura da cewa a Jihar Katsina da akwai yara waɗanda basu zuwa makaranta su kuma ne ke ta gararanba kan titunan manyan garuruwa a faɗin Jihar saboda lamarin da ya shafi ta’addanci da sauran laifuka. Da yake basu da wani wuri takamimi da aka ware masu domin su zauna a duk faɗin Jihar, yawanci suna zama ne da danginsu waɗanda suke a manyan garuruwa,ya yin da wasu suke zuwa makarantu ko wasu gine- gine ma mutane,irin hakan ko shakka babu yna shafar ilkimin yara a wasu makarantu.

Bada daɗewa bane mutanen da suka rasa matsugunin su daga wurare 12 daga ƙananan hukumomin Bakorı da Faskari waɗanda aka tilasta ma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaNeja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Next Post

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

17 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

19 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

22 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

23 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

23 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

1 day ago
Next Post
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.