• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Yarda Da Kai Ya Sa Wasu Kasashen Yamma Ke Neman Ta Da Matsaloli

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Rashin Yarda Da Kai Ya Sa Wasu Kasashen Yamma Ke Neman Ta Da Matsaloli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin babban kwamishina mai kula da aikin kare hakkin dan Adam na MDD ya gabatar da wani rahoto dangane da jihar Xijiang ta kasar Sin a kwanan baya, wanda ya nuna al’adar kasar Amurka da wasu kawayenta ta neman yin amfani da batun hakkin dan Adam a matsayin wani makami.

Me ya sa a ce haka?
Saboda da farko dai, yadda aka tsara rahoton ya saba ka’idoji. A matsayinsa na daya daga cikin hukumomin MDD, ya kamata ofishin babban kwamishina mai kula da hakkin dan Adam ya gudanar da duk wani aiki ne bisa iznin da majalisar kare hakkin dan Adam ta ba shi, kuma ba tare da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wata kasa ba.

  • Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

Amma ofishin ya gabatar da wannan rahoto kai tsaye, ba tare da neman samun izini ba, kuma bai taba neman sauraron ra’ayin Sin ba. Kana ta wannan hanya ya tsoma baki cikin harkokin gida na kasar Sin.

Na biyu, shi ne bayanan dake cikin rahoton sun saba da sanarwar da Madam Veronica Bachelet, babbar kwamishinar mai kula da aikin kare hakkin dan Adam ta MDD, ta gabatar, a ranar 28 ga watan Mayun bana, bayan da ta kammala ziyararta a jihar Xinjiang ta kasar Sin.

Inda ta yaba da kasar Sin, kan kokarinta a fannonin rage talauci, da kare mutane marasa karfi, da yunkurin tabbatar da ingancin hakkin dan Adam, da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Hakika idan mun yi nazari kan mutanen da suke aiki a ofishin babban kwamishina mai kula da aikin hakkin dan Adam, za a fahimci cewa, zai yi wahala wannan ofishi ya gabatar da wani rahoto na gaskiya.

Saboda kasar Amurka da wasu kawayenta sun tura ‘yan korensu don su zama manyan jami’an ofishin, inda su kan yin amfani da wasu bayanai marasa gaskiya wajen tsara rahotannin da suke haifar da matsin lamba ga kasar Sin, da sauran kasashe masu tasowa.

Amma me ya sa kasar Amurka da abokanta ke kokarin yin amfani da damammaki daban daban wajen shafa kashin kaza ga kasar Sin, da kafa shingaye ga sauran kasashen masu tasowa?

A ganina, suna haka ne domin ba su yarda da kansu ba.
Kasashen yammacin duniya na ganin cewa, dole ne kasashe masu tasowa su bi tsarin dimokuradiya irin nasu, da zama karkashin jagorancinsu, kafin su iya samun ci gaba mai dorewa.

Sai dai kasar Sin, a karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta zabi hanyar da ta tsara da kanta kuma da dace da yanayin al’ummarta, inda ta dauki tsarin gurguzu mai siffar musamman ta Sin, tare da samun babban ci gaba, cikin gomman shekarun da suka wuce.

Wannanya sa kasashen yamma kaduwa, saboda yadda kasar Sin ta samu nasara ta nuna cewa, kasashe masu tasowa za su iya raya kansu, ta hanyar musamman da suka zaba, maimakon ci gaba da bin umarnin kasashen yamma.

Wannan damuwa ta sa kasar Amurka da wasu kawayenta ke kokarin gogayya da kasar Sin, da haifar da matsaloli a harkoki masu alaka da hakkin dan Adam, da jihar Xinjiang, da yankin Taiwan na kasar Sin, da dai sauransu, don hana kasar Sin samun ci gaba. Sai dai kasar Sin ta yi ta samun nasarar daidaita wadannan matsaloli, bisa cikakken imanin da take da shi a kan turbar da ta zaba. Haka kuma Sinawa suna iya hakuri da mabambantan ra’ayoyin da ake samu a duniya, da iya tinkarar duk wani kalubalen da suka kunno kai yayin da suke kokarin raya kasarsu.

A nasu bangare, kasashe masu tasowa su ma sun fara ganin yanayin rashin adalci na tsare-tsaren kula da harkokin duniya da kasashen yamma suka gabatar, wannan ya sa suke kokarin nemo hanyar raya kansu wadda ta dace da yanayin da suke ciki.

Wannan wani muhimmin yanayi ne da muke fuskanta a wannan zamanin da muke ciki. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Karɓe Ofisoshin Yaƙin Zaɓen Buhari A Katsina

Next Post

Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

7 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

9 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

9 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

13 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

15 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

15 hours ago
Next Post
Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas

Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.