• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Yarda Da Kai Ya Sa Wasu Kasashen Yamma Ke Neman Ta Da Matsaloli

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Rashin Yarda Da Kai Ya Sa Wasu Kasashen Yamma Ke Neman Ta Da Matsaloli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin babban kwamishina mai kula da aikin kare hakkin dan Adam na MDD ya gabatar da wani rahoto dangane da jihar Xijiang ta kasar Sin a kwanan baya, wanda ya nuna al’adar kasar Amurka da wasu kawayenta ta neman yin amfani da batun hakkin dan Adam a matsayin wani makami.

Me ya sa a ce haka?
Saboda da farko dai, yadda aka tsara rahoton ya saba ka’idoji. A matsayinsa na daya daga cikin hukumomin MDD, ya kamata ofishin babban kwamishina mai kula da hakkin dan Adam ya gudanar da duk wani aiki ne bisa iznin da majalisar kare hakkin dan Adam ta ba shi, kuma ba tare da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wata kasa ba.

  • Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

Amma ofishin ya gabatar da wannan rahoto kai tsaye, ba tare da neman samun izini ba, kuma bai taba neman sauraron ra’ayin Sin ba. Kana ta wannan hanya ya tsoma baki cikin harkokin gida na kasar Sin.

Na biyu, shi ne bayanan dake cikin rahoton sun saba da sanarwar da Madam Veronica Bachelet, babbar kwamishinar mai kula da aikin kare hakkin dan Adam ta MDD, ta gabatar, a ranar 28 ga watan Mayun bana, bayan da ta kammala ziyararta a jihar Xinjiang ta kasar Sin.

Inda ta yaba da kasar Sin, kan kokarinta a fannonin rage talauci, da kare mutane marasa karfi, da yunkurin tabbatar da ingancin hakkin dan Adam, da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Hakika idan mun yi nazari kan mutanen da suke aiki a ofishin babban kwamishina mai kula da aikin hakkin dan Adam, za a fahimci cewa, zai yi wahala wannan ofishi ya gabatar da wani rahoto na gaskiya.

Saboda kasar Amurka da wasu kawayenta sun tura ‘yan korensu don su zama manyan jami’an ofishin, inda su kan yin amfani da wasu bayanai marasa gaskiya wajen tsara rahotannin da suke haifar da matsin lamba ga kasar Sin, da sauran kasashe masu tasowa.

Amma me ya sa kasar Amurka da abokanta ke kokarin yin amfani da damammaki daban daban wajen shafa kashin kaza ga kasar Sin, da kafa shingaye ga sauran kasashen masu tasowa?

A ganina, suna haka ne domin ba su yarda da kansu ba.
Kasashen yammacin duniya na ganin cewa, dole ne kasashe masu tasowa su bi tsarin dimokuradiya irin nasu, da zama karkashin jagorancinsu, kafin su iya samun ci gaba mai dorewa.

Sai dai kasar Sin, a karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta zabi hanyar da ta tsara da kanta kuma da dace da yanayin al’ummarta, inda ta dauki tsarin gurguzu mai siffar musamman ta Sin, tare da samun babban ci gaba, cikin gomman shekarun da suka wuce.

Wannanya sa kasashen yamma kaduwa, saboda yadda kasar Sin ta samu nasara ta nuna cewa, kasashe masu tasowa za su iya raya kansu, ta hanyar musamman da suka zaba, maimakon ci gaba da bin umarnin kasashen yamma.

Wannan damuwa ta sa kasar Amurka da wasu kawayenta ke kokarin gogayya da kasar Sin, da haifar da matsaloli a harkoki masu alaka da hakkin dan Adam, da jihar Xinjiang, da yankin Taiwan na kasar Sin, da dai sauransu, don hana kasar Sin samun ci gaba. Sai dai kasar Sin ta yi ta samun nasarar daidaita wadannan matsaloli, bisa cikakken imanin da take da shi a kan turbar da ta zaba. Haka kuma Sinawa suna iya hakuri da mabambantan ra’ayoyin da ake samu a duniya, da iya tinkarar duk wani kalubalen da suka kunno kai yayin da suke kokarin raya kasarsu.

A nasu bangare, kasashe masu tasowa su ma sun fara ganin yanayin rashin adalci na tsare-tsaren kula da harkokin duniya da kasashen yamma suka gabatar, wannan ya sa suke kokarin nemo hanyar raya kansu wadda ta dace da yanayin da suke ciki.

Wannan wani muhimmin yanayi ne da muke fuskanta a wannan zamanin da muke ciki. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Karɓe Ofisoshin Yaƙin Zaɓen Buhari A Katsina

Next Post

Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas

Related

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

8 hours ago
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

9 hours ago
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

10 hours ago
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu
Daga Birnin Sin

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

11 hours ago
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani
Daga Birnin Sin

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

12 hours ago
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
Daga Birnin Sin

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

1 day ago
Next Post
Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas

Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.