• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Ta Fannin Sauya Fasalin Makamashi A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Ta Fannin Sauya Fasalin Makamashi A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A inda a baya ake hakar kwal a birnin Datong na lardin Shanxi da ke arewacin kasar Sin, yanzu haka, an kafa jerin farantan samar da wutar lantarki ta hasken rana, wadanda tun bayan da suka fara aiki a shekarar 2016, sun samar da wutar lantarki da ta zarce KWH biliyan 12.

 

Lardin Shanxi da ke arewacin kasar Sin lardi ne da aka fi yawan samun kwal a kasar Sin. Sai dai yayin da ra’ayin nan na samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba ke kara zame wa al’ummar kasar jini da tsoka, a wannan yankin da Allah ya albarkace shi da kwal, ana ta samun sauye-sauye ta fannin nau’o’in makamashin da ake amfani da su. Bayan da kasar Sin ta fara gwajin yi wa fasalin makamashin gyare-gyare a lardin Shanxi a shekarar 2019, fasalin makamashi ya dinga kyautata a lardin, inda aka yi ta bunkasa samar da nau’o’in makamashi da ba za su gurbata muhalli ba, ciki har da lantarki da aka samar ta iska da rana da sauransu. Tun farkon lokacin da aka kaddamar da gwajin, wutar lantarki da aka iya samarwa ta iska da zafin rana ya zarce KW miliyan 20, amma ya zuwa karshen watan Yunin bana, adadin ya zarce KW miliyan 55.

  • Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon
  • Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Borno

Abin da ya faru a lardin Shanxi na daga cikin sauye-sauyen da ke faruwa a kasar Sin ta fannin tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba. Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, fadin dazuzzukan da aka dasa a kasar Sin ya kasance na farko a duniya, kuma kasar ita ce kasar da dazuzzukanta suka fi saurin karuwa a duniya, karuwar da ta kai kimanin kaso 1/4 na duk duniya cikin shekaru kusan 20 da suka wuce. Baya ga haka, a bara, karuwar yawan wutar lantarki da ake iya samarwa ta hasken rana da karfin iska da ma sauran nau’o’in makamashi masu tsabta a kasar Sin ta ninka ta kasashen kungiyar G7 har sau hudu, ta kuma ninka ta sauran kasashen duniya gaba daya fiye da sau biyu.

 

Labarai Masu Nasaba

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Sauye-sauyen sun kuma yi daidai da ra’ayin da David Wallace-Wells ya bayyana a cikin makalar da ya wallafa a jaridar New York Times, inda ya ce, kasar Sin tana kan gaba a duniya a kokarin da ake yi na gyara yanayin da ake ciki na yawan fitar da hayaki Carbon, ya kuma misalta jerin nasarorin da kasar Sin ta cimma a wannan fanni. Ya ce, a shekarar 2023, yawan wutar lantarki da ake iya samarwa ta zafin rana ta kai GW425 a fadin duniya, sai dai adadin zai ragu har zuwa GW 162 kawai idan an cire na kasar Sin, wanda ya kai GW 263. A cikin shekaru biyar da suka wuce kuma, yawan wutar lantarki da ake iya samarwa ta zafin rana ya ninku sau takwas, a yayin da adadi na sauran sassan duniya bai kai ninki.

 

A makalarsa, Mr.Wallace-Wells ya nuna yabo musamman kan rawar da kasar Sin ke takawa wajen taimakawa sauran sassan duniya rage fitar da iskar Carbon. Abin hakan yake, a cikin shekaru 10 da suka wuce, kasar Sin ta zamanto ta farko a duniya a fannin samar da sabbin makamashi, hakan ya sanya, sabbin makamashi zama wani muhimmin bangaren da kasar Sin ke aiwatar da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka. A yankin De Aar da ke tsakiyar kasar Afirka ta Kudu, na’urorin samar da wutar lantarki ta karfin iska, suna samar da wutar lantarki sama da KWH miliyan 750 a kowace shekara, kuma ta hakan an yi tsimin kwal kimanin tan sama da dubu 200, tare da rage fitar da iskar Carbon kimanin tan dubu 700. Sai kuma a yankin Garrisa na kasar Kenya, wani kamfanin kasar Sin ya kafa tashar samar da wutar lantarki ta zafin rana irinta mafi girma a gabashin Afirka, wanda ya sassauta matsalar karancin wutar lantarki da kasar ta fuskanta, kuma ba tare da fitar da iskar Carbon ba. A kasar Nijeriya, kamfanin kera bas bas na Yutong na kasar Sin, ya samar da bas bas masu aiki da wutar lantarki a birnin Lagos, wanda shi ne karo na farko da kasar ta fara samun wannan sabon nau’in motocin bas.

 

Mr.Wallace-Wells ya kuma bayyana damuwarsa game da yadda kasar Amurka da ma kawayenta suke kokarin dalike bunkasuwar kasar Sin ta fannin bunkasa sabbin makamashi, bisa dalilin cewa “kasar Sin na samar da kayayyaki masu alaka fiye da kima”, kuma a ganinsa, hakan zai iya haifar da koma baya ga kasar Sin a kokarinta na samar da sabbin makamashi, wanda daga karshe zai jefa duniya cikin mawuyacin hali. Ko da yake ba sai Mr.Wallace-Wells ya damu da hakan ba, sabo da kamar yadda takardar bayani kan sauyin fasalin makamashi da kasar Sin ta fitar a karshen watan da ya gabata ta ce, sauya fasalin makamashi ya zama dole ga kasar Sin. Kasar Sin na kokarin sauya fasalin makamashi ne ba don wani ya sa mu yi hakan ba, amma sabo da mu kanmu muke fatan yin haka, kuma wannan ba aikin da muke da zabi ba ne, amma aiki ne da dole mu yi.

 

Tinkarar sauyin yanayin duniya da dorewar makamashi na da alaka da makomar dan Adam. Kasar Sin na son yin kokari tare da kasa da kasa, su zurfafa hadin gwiwa ta fannin sauya fasalin makamashi, don tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin dan Adam.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Makamashi mai tsaftaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Sani Ya Sasanta Rigingimun Filaye 347 A Kaduna

Next Post

Kashin Shettima Ya Dawo Nijeriya Bayan Taron Majalisar Ɗinkin Duniya Na 79

Related

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

3 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

6 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

7 days ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Ra'ayi Riga

Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba

2 weeks ago
Next Post
Kashin Shettima Ya Dawo Nijeriya Bayan Taron Majalisar Ɗinkin Duniya Na 79

Kashin Shettima Ya Dawo Nijeriya Bayan Taron Majalisar Ɗinkin Duniya Na 79

LABARAI MASU NASABA

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.