• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Ta Fannin Sauya Fasalin Makamashi A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Ta Fannin Sauya Fasalin Makamashi A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A inda a baya ake hakar kwal a birnin Datong na lardin Shanxi da ke arewacin kasar Sin, yanzu haka, an kafa jerin farantan samar da wutar lantarki ta hasken rana, wadanda tun bayan da suka fara aiki a shekarar 2016, sun samar da wutar lantarki da ta zarce KWH biliyan 12.

 

Lardin Shanxi da ke arewacin kasar Sin lardi ne da aka fi yawan samun kwal a kasar Sin. Sai dai yayin da ra’ayin nan na samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba ke kara zame wa al’ummar kasar jini da tsoka, a wannan yankin da Allah ya albarkace shi da kwal, ana ta samun sauye-sauye ta fannin nau’o’in makamashin da ake amfani da su. Bayan da kasar Sin ta fara gwajin yi wa fasalin makamashin gyare-gyare a lardin Shanxi a shekarar 2019, fasalin makamashi ya dinga kyautata a lardin, inda aka yi ta bunkasa samar da nau’o’in makamashi da ba za su gurbata muhalli ba, ciki har da lantarki da aka samar ta iska da rana da sauransu. Tun farkon lokacin da aka kaddamar da gwajin, wutar lantarki da aka iya samarwa ta iska da zafin rana ya zarce KW miliyan 20, amma ya zuwa karshen watan Yunin bana, adadin ya zarce KW miliyan 55.

  • Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon
  • Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Borno

Abin da ya faru a lardin Shanxi na daga cikin sauye-sauyen da ke faruwa a kasar Sin ta fannin tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba. Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, fadin dazuzzukan da aka dasa a kasar Sin ya kasance na farko a duniya, kuma kasar ita ce kasar da dazuzzukanta suka fi saurin karuwa a duniya, karuwar da ta kai kimanin kaso 1/4 na duk duniya cikin shekaru kusan 20 da suka wuce. Baya ga haka, a bara, karuwar yawan wutar lantarki da ake iya samarwa ta hasken rana da karfin iska da ma sauran nau’o’in makamashi masu tsabta a kasar Sin ta ninka ta kasashen kungiyar G7 har sau hudu, ta kuma ninka ta sauran kasashen duniya gaba daya fiye da sau biyu.

 

Labarai Masu Nasaba

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Sauye-sauyen sun kuma yi daidai da ra’ayin da David Wallace-Wells ya bayyana a cikin makalar da ya wallafa a jaridar New York Times, inda ya ce, kasar Sin tana kan gaba a duniya a kokarin da ake yi na gyara yanayin da ake ciki na yawan fitar da hayaki Carbon, ya kuma misalta jerin nasarorin da kasar Sin ta cimma a wannan fanni. Ya ce, a shekarar 2023, yawan wutar lantarki da ake iya samarwa ta zafin rana ta kai GW425 a fadin duniya, sai dai adadin zai ragu har zuwa GW 162 kawai idan an cire na kasar Sin, wanda ya kai GW 263. A cikin shekaru biyar da suka wuce kuma, yawan wutar lantarki da ake iya samarwa ta zafin rana ya ninku sau takwas, a yayin da adadi na sauran sassan duniya bai kai ninki.

 

A makalarsa, Mr.Wallace-Wells ya nuna yabo musamman kan rawar da kasar Sin ke takawa wajen taimakawa sauran sassan duniya rage fitar da iskar Carbon. Abin hakan yake, a cikin shekaru 10 da suka wuce, kasar Sin ta zamanto ta farko a duniya a fannin samar da sabbin makamashi, hakan ya sanya, sabbin makamashi zama wani muhimmin bangaren da kasar Sin ke aiwatar da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka. A yankin De Aar da ke tsakiyar kasar Afirka ta Kudu, na’urorin samar da wutar lantarki ta karfin iska, suna samar da wutar lantarki sama da KWH miliyan 750 a kowace shekara, kuma ta hakan an yi tsimin kwal kimanin tan sama da dubu 200, tare da rage fitar da iskar Carbon kimanin tan dubu 700. Sai kuma a yankin Garrisa na kasar Kenya, wani kamfanin kasar Sin ya kafa tashar samar da wutar lantarki ta zafin rana irinta mafi girma a gabashin Afirka, wanda ya sassauta matsalar karancin wutar lantarki da kasar ta fuskanta, kuma ba tare da fitar da iskar Carbon ba. A kasar Nijeriya, kamfanin kera bas bas na Yutong na kasar Sin, ya samar da bas bas masu aiki da wutar lantarki a birnin Lagos, wanda shi ne karo na farko da kasar ta fara samun wannan sabon nau’in motocin bas.

 

Mr.Wallace-Wells ya kuma bayyana damuwarsa game da yadda kasar Amurka da ma kawayenta suke kokarin dalike bunkasuwar kasar Sin ta fannin bunkasa sabbin makamashi, bisa dalilin cewa “kasar Sin na samar da kayayyaki masu alaka fiye da kima”, kuma a ganinsa, hakan zai iya haifar da koma baya ga kasar Sin a kokarinta na samar da sabbin makamashi, wanda daga karshe zai jefa duniya cikin mawuyacin hali. Ko da yake ba sai Mr.Wallace-Wells ya damu da hakan ba, sabo da kamar yadda takardar bayani kan sauyin fasalin makamashi da kasar Sin ta fitar a karshen watan da ya gabata ta ce, sauya fasalin makamashi ya zama dole ga kasar Sin. Kasar Sin na kokarin sauya fasalin makamashi ne ba don wani ya sa mu yi hakan ba, amma sabo da mu kanmu muke fatan yin haka, kuma wannan ba aikin da muke da zabi ba ne, amma aiki ne da dole mu yi.

 

Tinkarar sauyin yanayin duniya da dorewar makamashi na da alaka da makomar dan Adam. Kasar Sin na son yin kokari tare da kasa da kasa, su zurfafa hadin gwiwa ta fannin sauya fasalin makamashi, don tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin dan Adam.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Makamashi mai tsaftaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Sani Ya Sasanta Rigingimun Filaye 347 A Kaduna

Next Post

Kashin Shettima Ya Dawo Nijeriya Bayan Taron Majalisar Ɗinkin Duniya Na 79

Related

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

18 hours ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

2 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

7 days ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

1 week ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

1 week ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 weeks ago
Next Post
Kashin Shettima Ya Dawo Nijeriya Bayan Taron Majalisar Ɗinkin Duniya Na 79

Kashin Shettima Ya Dawo Nijeriya Bayan Taron Majalisar Ɗinkin Duniya Na 79

LABARAI MASU NASABA

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.