• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Kasar Sin Ta Taka A Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Rawar Da Kasar Sin Ta Taka A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin ta riga ta zama babbar kasar da ke “samar da kyakkyawan tasiri, da ba da jagoranci wajen kirkiro sabbin fasahohi wadda ke sauke nauyin dake bisa wuyanta a duniya”. An tabbatar da wannan ra’ayi a wajen taron aikin diplomasiyya na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da ya gudana tsakanin ranar 27 zuwa 28 ga wata, a birnin Beijing na kasar Sin.

A wannan shekara, an samu barkewar wutar yaki tsakanin bangarorin Falasdinu da Isra’ila. Don neman kwantar da kurar da ta tashi, kasar Sin ta yi kokarin sulhuntawa tsakanin bangarori masu ruwa da tsaki.

  • Majalisar NPC Za Ta Fara Zaman Taron Shekara-shekara A Ranar 5 Ga Watan Maris
  • Xi Jinping Ya Gana Da Jakadun Kasar Sin Dake Kasashen Waje Wadanda Suka Dawo Beijing Don Halartar Taro

Duk da wannan shekarar da muke ciki, tattalin arzikin duniya na tafiyar hawainiya. Ganin haka ya sa kasar Sin ke kokarin raya tattalin arzikinta, don neman taimakawa farfadowar tattalin arzikin duniya.

A wannan shekara ta 2023, an samu cikar shekaru 45 da fara manufar bude kofa da gyare-gyare a gida a kasar ta Sin. Bisa hasashen da kungiyoyin kasa da kasa suka yi, kasar Sin za ta samar da kashi 1 cikin kashi 3 na gudunmawar da ta haifar da karuwar tattalin arzikin duniya.

Duk a wannan shekara, an samu cikar shekaru 10 da gabatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, kana tsarin BRICS da na SCO dukkansu sun habaka, yayin da kungiyar kasashen Afrika ta AU ta zama mambar kungiyar kasashe da yankuna 20 mafi karfin tattalin arziki (G20).

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

A karshen shekarar 2023, huldar dake tsakanin kasar Sin da ta Amurka ta daidaita, inda haduwar shugabannin kasashen 2 a San Francisco na kasar Amurka ta samar da karin tabbaci ga huldar kasa da kasa.

Ko da yake ana ta fuskantar matsaloli a wannan zamanin da muke ciki, amma a ganin kasar Sin, yanayin ci gaba na tarihin dan Adam, da hadewar gamayyar kasa da kasa, ba zai canza ba.

A shekarar 2023, kasar Sin ta sauke nauyin dake bisa wuyanta. Sa’an nan ana sa ran ganin kasar ta kulla hulda mafi kyau tare da sauran kasashe, da kokarin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya tare da su, a shekarar 2024 mai zuwa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

30 Watan Oktoba 2023: Messi Ya Lashe Gasar Ballon d’ Or

Next Post

Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Gaskiya Ta Bayyana Kan Bullar Mata Masu Shan Jini

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

17 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

18 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

19 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

20 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

21 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

1 day ago
Next Post
Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Gaskiya Ta Bayyana Kan Bullar Mata Masu Shan Jini

Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Gaskiya Ta Bayyana Kan Bullar Mata Masu Shan Jini

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

July 19, 2025
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

July 19, 2025
Abinci

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

July 19, 2025
sallah

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

July 19, 2025
Shettima

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

July 19, 2025
Fyade

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

July 19, 2025
APC

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

July 19, 2025
Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.