ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

by Abubakar Sulaiman
9 months ago

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 4 na Free on Board (FOB) da Hukumar Haraji ta Nijeriya (NCS) ta sanya a kan duk kayan da ake shigowa da su. Shugaban Ma’aikatar Kuɗi kuma Ministan Hada-hadar Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, ya bayyana wannan mataki bayan samun damuwa daga masu shigo da kaya, masana harkokin kasuwanci, da sauran masu ruwa da tsaki a masana’antu game da illar harajin ga tattalin arziki.

A wata wasiƙa da aka sanya wa hannu ranar Litinin, 15 ga Satumban 2025, da aka aika wa Kwaturola Janar na Kwastam, Mista Wale Edun, a matsayinsa na Shugaban Kwamitin NCS, ya umurci dakatar da harajin nan take.

Wasiƙar da Babban Sakataren Ma’aikatar Kuɗi kan Ayyuka na Musamman, Mista Raymond Omachi, ya
sanya wa hannu, ta bayyana cewa an gudanar da tattaunawa sosai da masu ruwa da tsaki da masana, inda
ra’ayinsu ya nuna cewa harajin zai kawo babbar matsala ga harkokin kasuwanci da tattalin arziki.

ADVERTISEMENT
  • Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
  • Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

“Bayan tattaunawa mai zurfi da masu ruwa da tsaki a masana’antu, masana harkokin kasuwanci, da
jami’an gwamnati masu dacewa suka yi, ya bayyana cewa aiwatar da wannan haraji zai haifar da manyan
ƙalubale ga sauƙaƙe harkokin kasuwanci, yanayin gudanar da harkokin kasuwanci, da kuma daidaiton
tattalin arziki gaba ɗaya,” in ji wasiƙar.

Masu ruwa da tsaki, musamman masu shigo da kaya da masu gudanar da kasuwanci, sun yi gargaɗi sau da yawa cewa harajin zai ƙara hauhawar farashi, ya sa kayan masarufi su yi tsada, kuma ya rage ƙarfin fafatawa na Nijeriya a kasuwannin duniya.
Da yawa kuma sun jayayya cewa wannan cajin zai ƙara wahalar da ƙoƙarin sauƙaƙe farashin gudanar da
kasuwanci a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

A cewar ma’aikatar, dakatarwar ta na nufin samar da damar ci gaba da tattaunawa da duk masu ruwa da
tsaki da kuma yin cikakkiyar bitar tsarin harajin da tasirinsa na dogon lokaci ga tattalin arziki.
A watan Afrilu 2025, Kwaturola Janar na Kwastom, Adeniyi, ya bayyana shirin sake gabatar da harajin
kashi 4 bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki, cewa wannan cajin, wanda ake lissafawa bisa Free on
Board (FOB) na kayan da ake shigowa da su, an riga an sokƙ shi a baya daga al’umma masu kasuwanci
saboda nauyinsa ga masu shigo da kaya.

Nan da nan sanarwar ta jawo cece-kuce daga ƴ an kasuwa, kamfanonin jigilar kaya, da ƙungiyoyin
masana’antu, waɗanda suka bayyana cewa matakin zai rage amincewar masu zuba jari kuma ya rage jan
hankalin da Nijeriya ke yi a matsayin cibiyar kasuwanci.

Ma’aikatar kuɗi ta fayyace cewa dakatarwar ba ta nufin soke harajin, sai dai mataki ne na dakatarwa
domin sake duba yiwuwar tasirin harajin. Ma’aikatar ta jaddada ƙudurin gwamnati na daidaita samun
kuɗaɗen shiga tare da bunƙasa tattalin arziki.

“Ma’aikatar Kuɗi na sa ran yin aiki kafaɗa da kafaɗa da Hukumar Haraji ta Nijeriya (NCS) da duk masu
ruwa da tsaki domin shirya tsarin samun kuɗaɗe cikin adalci da inganci wanda zai tallafa wa kuɗaɗen
gwamnati ba tare da lalata harkokin kasuwanci ko daidaiton tattalin arziki ba,” in ji sanarwar.

Haraji
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.