ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

30 Watan Oktoba 2023: Messi Ya Lashe Gasar Ballon d’ Or

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Ballon

A ranar 30 ga watan Oktoba na shekarar 2023, dan wasa Lionel Messi ya lashe kyutar gwarzon dan kwallon kafa na duniya na 2023, wato Ballon d’Or karo na takwas jimilla.

Messi tsohon dan wasan Barcelona da Paris St Germain mai buga wasa a Inter Miami a Amurka ya dauki kofin duniya a Katar a 2022, kofin da ya daukar wa Argentina na uku a tarihi. Messi, shi ne ya ja ragamar Argentina ta lashe babban kofin duniya na farko a wajensa, kuma na uku a kasar jimilla, sannan Aitana Bonmati ce ta zama gwarzuwar kwallon kafa ta 2023, wato macen da ta lashe Ballon d’Or.

  • Ci Gaba Da Gudanar Da Sha’Anin Da Mao Zedong Ya Kaddamar, Shi Ne Abu Mafi Dacewa Game Da Tunawa Da Shi
  • NAF Ta Lalata Haramtattun Wuraren Tace Mai Guda 6 A Ribas 

Bonmati, mai shekara 25, ta dauki Champions League da kofin Sifaniya a Barcelona a bara – da lashe kofin duniya a bana tare da tawagar Sifaniya. Sai Sam Kerr ta Chelsea da Australia ce ta biyu, sai ‘yar kwallon Barcelona da tawagar Sifaniya, Salma Paralluelo ce ta uku.

ADVERTISEMENT

Karo na takwas kenan da Messi ke lashe kyautar ta Ballon d’Or, bayan da ya dauka a 2009, 2010, 2011, 2012, 2015, 2019 da kuma 2021 sai dai ya lashe kyautar 2021 tare da Robert Lewandowski, ya kuma yi wa Cristiano Ronaldo tazara mai biyar da ya ci a 2008, 2013, 2014, 2016 da kuma 2017).

Masu uku-uku a tarihin karbar kyautar Ballon d”Or sun hada da Michel Platini da Marco ban Basten da kuma Johan Cruyff sai Karim Benzema wanda ya lashe kyautar a bara lokacin yana buga wasa a Real Madrid, a kakar da Messi bai kai bantensa ba cikin ‘yan takara.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Wasu na ganin Erling Haaland ne ya kamata ya lashe Ballon d’Or na bana, bayan da ya ci Champions League da Premier League da FA Cup a Manchester City a bara, sannan Haalan, tsohon dan wasan Borussia Dortmund ya ci kwallo 52 a wasann 53 a kakar da ta wuce.

Wasu da suka lashe kyautuka:

Haaland ya karbi kyautar Gerd Muller – kyauta ce saboda zun-zurutun kwallaye 52 da ya zura a raga a wasa 53 a kakar da ta wuce.

Bellingham ya lashe kyautar Kopa Trophy – kyauta ce ta matashin da ba kamarsa a duniya a 2023.

Binicius Jr, ya karbi kyautar Socrates – Dan kasar Brazil ya samu wannan lambar yabon sakamakon gidauniyarsa ta taimakawa yara marasa gata a kasarsa.

Emiliano Martinez ya lashe kyautar Yashin – Tsohon wanda ya buga wasan aro a Odford United, shi ne gwarzon mai tsaron raga a 2023. Manchester City ce kungiyar kwallon kafa ta maza da ba kamarta a bara. Kungiyar ta lashe kofin Champions League da Premier League da FA Cup a bara, sannan tana da ‘yan wasa bakwai daga 30 da suka yi takarar kyautar Ballon d’Or.

Kungiyar Barcelona ta mata ce kan gaba a bajinta a bana. Ta lashe Champions League a bara da kofin Sifaniya ‘yan wasanta shida suna cikin takarar Ballon d’Or bangaren mata.

Manchester City Ta Karya Tarihin United

Har ila yau, a ranar 22 ga watan Disamba na wannan shekarar kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta kammala lashe kofuna biyar bayan da tun farko ta kammala kakar wasan bana da kofuna uku a cikin jakarta inda ta lashe gasar firimiya da kofin kalubale da daukar kofin zakarun turai bayan ta doke Inter Milan da ci 1-0 a wasan karshe.

Wasan karshen da suka fafata da Inter Millan, sun buga wasan ne a filin Olympic na Atuturk da ke Istanbul a kasar Turkiyya inda dan wasa Rodri ya zura kwallon a raga.

Tun a watan Mayu kungiyar ta lashe kofuna biyu – na Gasar Firimiya ta Ingila da Gasar FA, kuma hakan na nufin ta zama kungiyar Turai ta biyu da ta lashe kofuna uku a kakar wasa daya – Manchester United ta kafa wannan tarihi a 1999.

Kazalika wannan bajinta ta Pep Guardiola ya jaddada matsayinsa na zama daya daga cikin koci mafi shahara inda ya ci kofinsa na uku na Zakarun Turai bayan ya lashe biyu a Barcelona, na karshe shi ne wanda ya dauka a 2011.

‘Yan wasan na Guardiola sun yi gumurzu sosai da ‘yan wasan Inter Milan, wadanda suka nuna matukar hazaka, sai dai a minti na 68 Rodri ya zura kwallon da ta ba su nasara.

Manchester City ta yi nasara ne duk da cewa zakakurin dan wasan tsakiyarta Kebin De Bruyne ya ji rauni kafin a tafi hutun rabin lokaci lamarin da ya sa aka cire shi daga wasan.

Spain Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

A ranar 20 ga watan Agusta na wannan shekarar ta 2023 kasar Spain ta lallasa Ingila a wasan karshe na cin kofin kwallon kafa na duniya na mata inda ta lashe kofin a karon farko a tarihi. Kwallon da ’yar wasa Olga Carmona ta ci a minti na 29 ce dai ta bai wa Sifaniya nasarar a wasan da aka fafata kuma an buga wasan ne a Sydney, Babban Birnin Kasar Austaraliya.

Tawagar ta kasar Sifaniya dai ta rike wuta ne tun daga farkon wasan, inda duk yunkurin da matan na Ingila suka yi na farke kwallon ya ci tura har aka tashi wasan.

’Yar wasan nan ta Sifaniya da ta taba lashe kambun Ballon d’Or ta duniya, Aledia Putellas dai an ajiye ta daga jerin ’yan wasan da suka buga wa kasarta wasan na karshe da Ingila.

‘Yan Wasan Da Suka Saudiya Daga Turai

Tun bayan komawar fitaccen dan wasan kwallon kafa Cristiano Ronaldo kasar Saudiyya da buga wasa bayan ya raba gari da kungiyar Manchester United, sai gasar kasar ta kara armashi a idon masoya kwallo.

A wannan shekarar an samu kwararar ‘yan wasa da dama daga turai zuwa kasar ta Saudiyya, wasu daga cikin ‘yan wasan ma babu wanda ya yi tunanin cewa za su dauki matakin canja sheka zuwa kasar ta Saudiyya saboda ana ganin akwai sauran lokaci.

Sai dai a daidai lokacin da za a fara kakar bana, kungiyoyin kasar sun rikita kasuwar hada-hadar ’yan wasa, inda suka yi ta taya manyan fitattun ’yan wasan duniya da kudi mai yawa kuma suka dinga tafiya.

Dan wasan kasar Senegal Koulibaly ya bayyana cewa saboda kasancewar yana bukatar kudi sosai da zai ci gaba da daukar dawaniniyar iyalansa da ’yan uwansa da kuma wasu ayyuka da yake so ya yi a kauyen da ya fito, da kuma kasancewarsa Musulmi ne suka sa ya yanke shawarar komawa Saudiyya da buga kwallo.

Wani abu da ya tayar da kura shi ne yadda dan wasa Cristiano Ronaldo ya yi Sujjada bayan zura kwallo a wani wasa a kasar, inda aka rika yada hoton Sujjadar ana bayanai a kai

Karim Benzema: Daga Real Madrid zuwa Al Ittihad Karim Benzema, wanda shi ne Gwarzon dan kwallon duniya na yanzu ya bar kungiyar Real Madrid ta Sifaniya duk da cewa sun bukaci ya kara sanya hannu a kwantaragi domin ci gaba da zama kungiyar inda ya koma Al Ittihad ta Saudiyya.

Barin Real Madrid ya yi matukar zuwa wa magoya bayan kungiyar da ba-zata, kasancewar shi ne Kyaftin, sannan ba a samu shakku ba a kan kasancewarsa wanda yake jan ragamar kungiyar, ballanta a fara tunanin ajiye shi a benci. Ya koma kungiyar Al Ittihad ce wadda ta lashe Gasar Firimiyar Saudiyya ta bara, inda ya sanya hannu a kwantaragin shekara uku a kan Fam miliyan 107 duk shekara, kudin da suka ninka kudin da yake samu a Real Madrid.

Da yake bayani a lokacin gabatar da shi ga magoya bayan kungiyar, Karim farawa ya yi da sallama, sannan ya ce a matsayinsa na Musulmi ya ji dadin komawa Saudiyya da buga wasa, sannan ya ce kasancewar Cristiano Ronaldo, wanda ya bayyana a matsayin abokinsa a gasar kasar ya sa ya samu saukin yanke shawarar.

Ballon
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
Wasanni

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Next Post
Rawar Da Kasar Sin Ta Taka A Duniya

Rawar Da Kasar Sin Ta Taka A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.