• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

Ce-ce-ku-cen Da Aka Yi Kan Yawan Wakilan Nijeriya 

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta taka muhimmiyar rawa a taron dumamar yanayi na duniya (COP28), wanda ya gudana a Kasar Dubai.

Sai dai, ana ta faman caccakar gwamnatin tarayya dangane da yawan tawagar da suka wakilci Nijeriya a wannan babban taron.

  • An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

An rawaito cewa, Kasar Nijeriya ta tura wakilai har mutum 1,411, wadda ta kasance kasa ta uku a yawan kasashen da suka tura, domin halartar wannan taro.

Lamarin ya gamu da suka kwarai da gaske, musamman ganin yadda al’ummar Nijeriya ke ta fama da halin kaka-na-ka-yi, sakamakon halin matsatsin rayuwa da aka samu kai a ciki, tun bayan janye tallafin mai, inda masu ruwa da tsaki kuma suka soki matakin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu; kan wannan lamari.

A gefe guda kuma, Fadar Shugaban Kasa ta yi karin haske a kan wakilai 1,411, inda ta ce wadanda gwamnatin tarayya ta dauki nauyi, ba su kai mutum 100 a cikinsu ba.

Labarai Masu Nasaba

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Da yake tofa nasa albarkacin bakin, Dan Takarar Shugaban Kasa na Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya zargi Shugaba Tinubu da yin amfani da wannan taro na sauyin yanayi zuwa taron jam’iyya, a daidai irin wannan lokaci da al’ummar Nijeriya ke neman tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Abubukar, a wata sanarwa da ke dauke da sa hannun Kakakinsa, Paul Ibe, ya kuma zargi Tinubu da barnatar da dukiyar kasa; duk kuwa da halin matsin da kasar ke ciki. Ya kara da cewa, duk gwamnatin da ta san abin da take yi, musamman a irin wannan lokacin, ba za ta taba fara yin yunkurin tura wakilai har sama da dubu wani taro ba.

Haka nan shi ma dan takarar Jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana yawan wakilai a matsayin asarar dukiyar al’ummar kasa.

A shafin Obin na Tiwita, ya ce, mafi yawan wadanda aka tura a matsayin wakilan, ba su da wata alaka da aikin gwamnati.

“Mafi yawan wadanda aka tura, babu abin da suka sani dangane da sauyin yanayi,” kamar yadda ya zarga.

Sannan, ya yi tir da matakin da cewa; a irin lokacin da al’ummar Nijeriya ke kan gwagwarmayar neman abincin da za su kai baki tare da matsin rayuwa da ya yi musu katutu, sai ga shi wannan gwamnati ta kwashi makuden kudade ta tura tulin wakilai zuwa wani taro a kasar waje.

Da yake mai da nasa martanin, babban mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren yada labarai, Temitope Ajayi, a wata sanarwar da ya fitar, ya bayyana cewa; ba dukkanin wakilan Nijeriya 1,411 a taron COP28 ne gwamnati ta dauki nauyinsu ba.

Ya ce, wakilan Nijeriya sun hada da bangarorin fararen hula, shugabannin ‘yan kasuwa, kwararru a bangaren muhalli, masana kan yanayi, ‘yan jarida da kuma jami’an gwamnati daga ma’aikatu da sassa daban-daban.

Duk da dai, bai bayyana adadin jami’an da gwamnatin ta dauki nauyin biyan kudin tafiyar tasu taron ba, sabanin jita-jitan da ake cewa; sun kai sama da wakilai 600 da gwamnati ta dauki nauyinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: COP28DubaiTawagar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Next Post

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

Related

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

1 hour ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

3 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

3 hours ago
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89
Labarai

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

3 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

6 hours ago
Ministan Tsaro
Labarai

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

8 hours ago
Next Post
Game Da Tambayar Nan:  Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

LABARAI MASU NASABA

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.