• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

Ce-ce-ku-cen Da Aka Yi Kan Yawan Wakilan Nijeriya 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta taka muhimmiyar rawa a taron dumamar yanayi na duniya (COP28), wanda ya gudana a Kasar Dubai.

Sai dai, ana ta faman caccakar gwamnatin tarayya dangane da yawan tawagar da suka wakilci Nijeriya a wannan babban taron.

  • An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

An rawaito cewa, Kasar Nijeriya ta tura wakilai har mutum 1,411, wadda ta kasance kasa ta uku a yawan kasashen da suka tura, domin halartar wannan taro.

Lamarin ya gamu da suka kwarai da gaske, musamman ganin yadda al’ummar Nijeriya ke ta fama da halin kaka-na-ka-yi, sakamakon halin matsatsin rayuwa da aka samu kai a ciki, tun bayan janye tallafin mai, inda masu ruwa da tsaki kuma suka soki matakin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu; kan wannan lamari.

A gefe guda kuma, Fadar Shugaban Kasa ta yi karin haske a kan wakilai 1,411, inda ta ce wadanda gwamnatin tarayya ta dauki nauyi, ba su kai mutum 100 a cikinsu ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

Da yake tofa nasa albarkacin bakin, Dan Takarar Shugaban Kasa na Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya zargi Shugaba Tinubu da yin amfani da wannan taro na sauyin yanayi zuwa taron jam’iyya, a daidai irin wannan lokaci da al’ummar Nijeriya ke neman tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Abubukar, a wata sanarwa da ke dauke da sa hannun Kakakinsa, Paul Ibe, ya kuma zargi Tinubu da barnatar da dukiyar kasa; duk kuwa da halin matsin da kasar ke ciki. Ya kara da cewa, duk gwamnatin da ta san abin da take yi, musamman a irin wannan lokacin, ba za ta taba fara yin yunkurin tura wakilai har sama da dubu wani taro ba.

Haka nan shi ma dan takarar Jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana yawan wakilai a matsayin asarar dukiyar al’ummar kasa.

A shafin Obin na Tiwita, ya ce, mafi yawan wadanda aka tura a matsayin wakilan, ba su da wata alaka da aikin gwamnati.

“Mafi yawan wadanda aka tura, babu abin da suka sani dangane da sauyin yanayi,” kamar yadda ya zarga.

Sannan, ya yi tir da matakin da cewa; a irin lokacin da al’ummar Nijeriya ke kan gwagwarmayar neman abincin da za su kai baki tare da matsin rayuwa da ya yi musu katutu, sai ga shi wannan gwamnati ta kwashi makuden kudade ta tura tulin wakilai zuwa wani taro a kasar waje.

Da yake mai da nasa martanin, babban mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren yada labarai, Temitope Ajayi, a wata sanarwar da ya fitar, ya bayyana cewa; ba dukkanin wakilan Nijeriya 1,411 a taron COP28 ne gwamnati ta dauki nauyinsu ba.

Ya ce, wakilan Nijeriya sun hada da bangarorin fararen hula, shugabannin ‘yan kasuwa, kwararru a bangaren muhalli, masana kan yanayi, ‘yan jarida da kuma jami’an gwamnati daga ma’aikatu da sassa daban-daban.

Duk da dai, bai bayyana adadin jami’an da gwamnatin ta dauki nauyin biyan kudin tafiyar tasu taron ba, sabanin jita-jitan da ake cewa; sun kai sama da wakilai 600 da gwamnati ta dauki nauyinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: COP28DubaiTawagar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Next Post

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

Related

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

32 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

1 hour ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

6 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

15 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

16 hours ago
Next Post
Game Da Tambayar Nan:  Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.