ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

Ce-ce-ku-cen Da Aka Yi Kan Yawan Wakilan Nijeriya 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Dumamar Yanayi

Nijeriya ta taka muhimmiyar rawa a taron dumamar yanayi na duniya (COP28), wanda ya gudana a Kasar Dubai.

Sai dai, ana ta faman caccakar gwamnatin tarayya dangane da yawan tawagar da suka wakilci Nijeriya a wannan babban taron.

  • An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

An rawaito cewa, Kasar Nijeriya ta tura wakilai har mutum 1,411, wadda ta kasance kasa ta uku a yawan kasashen da suka tura, domin halartar wannan taro.

ADVERTISEMENT

Lamarin ya gamu da suka kwarai da gaske, musamman ganin yadda al’ummar Nijeriya ke ta fama da halin kaka-na-ka-yi, sakamakon halin matsatsin rayuwa da aka samu kai a ciki, tun bayan janye tallafin mai, inda masu ruwa da tsaki kuma suka soki matakin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu; kan wannan lamari.

A gefe guda kuma, Fadar Shugaban Kasa ta yi karin haske a kan wakilai 1,411, inda ta ce wadanda gwamnatin tarayya ta dauki nauyi, ba su kai mutum 100 a cikinsu ba.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Da yake tofa nasa albarkacin bakin, Dan Takarar Shugaban Kasa na Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya zargi Shugaba Tinubu da yin amfani da wannan taro na sauyin yanayi zuwa taron jam’iyya, a daidai irin wannan lokaci da al’ummar Nijeriya ke neman tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Abubukar, a wata sanarwa da ke dauke da sa hannun Kakakinsa, Paul Ibe, ya kuma zargi Tinubu da barnatar da dukiyar kasa; duk kuwa da halin matsin da kasar ke ciki. Ya kara da cewa, duk gwamnatin da ta san abin da take yi, musamman a irin wannan lokacin, ba za ta taba fara yin yunkurin tura wakilai har sama da dubu wani taro ba.

Haka nan shi ma dan takarar Jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana yawan wakilai a matsayin asarar dukiyar al’ummar kasa.

A shafin Obin na Tiwita, ya ce, mafi yawan wadanda aka tura a matsayin wakilan, ba su da wata alaka da aikin gwamnati.

“Mafi yawan wadanda aka tura, babu abin da suka sani dangane da sauyin yanayi,” kamar yadda ya zarga.

Sannan, ya yi tir da matakin da cewa; a irin lokacin da al’ummar Nijeriya ke kan gwagwarmayar neman abincin da za su kai baki tare da matsin rayuwa da ya yi musu katutu, sai ga shi wannan gwamnati ta kwashi makuden kudade ta tura tulin wakilai zuwa wani taro a kasar waje.

Da yake mai da nasa martanin, babban mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren yada labarai, Temitope Ajayi, a wata sanarwar da ya fitar, ya bayyana cewa; ba dukkanin wakilan Nijeriya 1,411 a taron COP28 ne gwamnati ta dauki nauyinsu ba.

Ya ce, wakilan Nijeriya sun hada da bangarorin fararen hula, shugabannin ‘yan kasuwa, kwararru a bangaren muhalli, masana kan yanayi, ‘yan jarida da kuma jami’an gwamnati daga ma’aikatu da sassa daban-daban.

Duk da dai, bai bayyana adadin jami’an da gwamnatin ta dauki nauyin biyan kudin tafiyar tasu taron ba, sabanin jita-jitan da ake cewa; sun kai sama da wakilai 600 da gwamnati ta dauki nauyinsu.

Dumamar Yanayi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Game Da Tambayar Nan:  Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.