• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

by Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da kasashe masu tasowa ke fuskantar wariya kamar wata saniyar ware daga takwarorinsu na kasashen yamma da Amurka a gefe guda, sai ga wata guguwa mai karfi dauke da hadin gwiwar kasashen BRICS ta taso da nufin samar da daidaito, ‘yancin kasashe masu tasowa tare da kiran sauya fasali a tsare-tsaren yadda ake gudanar da harkoki na kasa da kasa.

Wannan guguwa ta yi nasara sosai, inda taron kolin kungiyar BRICS na bana karo na 17 da aka yi a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil, ya tayar wa shugaban Amurka da hankali, wanda ya yi barazanar kara kakaba harajin kaso 10% kan kasashen dake goyon bayan sukar muradunta na “kama karya”. Wannan sai ya tuna min da wani karin maganar da Hausawa ke cewa, “wane dare ne, Jemage bai gani ba.”

  • Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC
  • Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

Yayin da yanayin dangantakar kasa da kasa ke fuskantar kalubale da sauye-sauye masu yawa, kasashen BRICS suna kara samun karbuwa a matsayin kungiya mai rajin yin kwaskwarima ga tsarin gudanar harkoki na kasa da kasa domin samar da duniya mai tattare da mutunta juna da adalci.

Duba da hakan ne, a yayin taron kolin, firaministan kasar Sin Li Qiang ya yi kira da cewa, “ya kamata kasashen BRICS su zage damtse wajen ganin sun ci gaba da yin gyare-gyare a tsarin gudanar harkoki na duniya, kuma Sin a shirye take ta hada gwiwa da sauran kasashen BRICS, domin sa kaimi ga gudanar da harkokin duniya cikin adalci, da daidaito, da inganci da tsari, da yin aiki tare domin gina ingantacciyar duniya.”

Jawabin na Li ya sake jaddada aniyar kasar Sin na karfafa kasashen BRICS a matsayin babbar hanyar yin gyare-gyare kan tsarin gudanar harkokin duniya. A matsayinta na wakiliyar muryar kasashe masu tasowa, BRICS na tattare da burika na sauya fasalin yadda ake gudanar da harkokin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

Shi ma Uban taro mai masaukin baki, shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya bayyana a jawabinsa na taron kolin cewa, “Idan har ba a samu sauyi a tsarin gudanar da harkokin kasa da kasa a wannan karni na 21 ba, to ya zama wajibi kasashen BRICS su taimaka wajen ganin an sabunta shi.”

BRICS taska ce ta hadin kai, daidaito da kuma kokarin tafiya tare don samun ci gaba da tsira tare, da kuma karfafawa kasashe masu neman ‘yancin fadin albarkacin bakinsu a harkokin tsare-tsare na hadin kan kasashen duniya.

Taron kolin kungiyar na bana, na zuwa ne a daidai lokacin da kasuwannin duniya ke cike da firgici biyo bayan yakin cinikayya da kasar Amurka ta kaddamar, amma BRICS ta tsaya tsayin daka wajen inganta harkokin tattalin arziki, inda kungiyar ke samar da wani dandali na bai daya da ke tallafawa cinikayya a kasashe daban-daban, da inganta cinikayyar a tsakaninsu, wanda hakan ya ba su damar bunkasa amfani da kudaden cikin gida, don rage dogaro kan wasu kasuwanni masu iyaka.

Yayin da kasashe da dama ke nuna sha’awar shiga kungiyar, hakan na nuni da tasiri da nasarar da kungiyar ke samu cikin sauri, saboda ta bayyana gaskiya da adalci a fili, ta inganta tsarin dimokuradiyyar duniya, kowa yana da ‘yancin fadi a ji.

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

Next Post

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Related

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

3 days ago
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

4 days ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

6 days ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

1 week ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

2 weeks ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 weeks ago
Next Post
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

October 3, 2025
Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.