• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin

by Sulaiman
3 weeks ago
in Daga Birnin Sin
0
Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bude taron inganta karfin al’adun kasar Sin na 2025, jiya Litinin a Shenzhen na lardin Guangdong, lamarin dake nuna yadda Sin ke dagewa wajen karfafa al’adunta.

A matsayinta na wadda na kan kira da “mai jagorantar zamanintar da duniya”, kare al’adunta na gargajiya wani bangare ne na sirrin ci gaban kasar Sin har ma da zamanintar da kanta.

  • Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
  • Gwamnatin Kano Zata Gina Masallacin Da Aka Ƙona Masallata A Gezawa

Idan ana batu na zamani da fasahohi, to kowa ya san Sin ce a kan gaba, sai dai duk da hakan, ko kadan ba ta yi watsi da al’adunta na gargajiya ba, asali ma, al’adun da akidun da suka samo asali daga kaka da kakanni, su ne ke jagorantar ayyukan raya kasa da ci gaban da Sin ke samu. A nan kasar Sin na fahimci cewa, wayewa ko ci gaba, ba shi ne yin watsi da al’adu ba, wayewa shi ne rike asalinka da kokarin raya shi da ma alfahari da shi.

Wannan taro da aka bude a jiya Litinin, ya hada masana da ’yan kasuwa da masu tsara manufofi, domin samar da wani dandali na musayar ra’ayi da basirar kara yayatawa da kare al’adun gargajiya na kasar Sin. Hakan ya nuna cewa, duk da wanzuwar al’adun a zukatan jama’a da yadda suke daukar su da muhimmanci, kasar Sin tana son kara karfinta a wannan bangare domin ci gaba ya raya shi ba tare da tsayawa ba.

Al’adu su ne ke nuna asalin kasa da al’ummarta, kuma shi ke hada kan al’ummar su zama tsintsiya madaurinki daya. A duniyar dake dunkulewa, abu ne mai muhimmanci a rike al’adu domin ci gaba da raya kasa da tabbatar da kasantuwarta. Kamar yadda na fada a baya, kare al’adun na daya daga cikin jigon ci gaban kasar Sin, inda ake iya ganin hakan cikin dukkanin manufofi da dabarunta na raya kasa.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Ya zama wajibi duk wata kasa dake son samun ci gaba mai dorewa, ta rike asalinta, ta kare al’adunta, ta zabar wa kanta hanya mafi dacewa da ita kamar yadda kasar Sin ta yi, domin har kullum, Sin za ta ci gaba da zama abin koyi ga sauran sassan duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno

Related

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

2 hours ago
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575
Daga Birnin Sin

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

4 hours ago
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

4 hours ago
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

5 hours ago
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

22 hours ago
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda
Daga Birnin Sin

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

22 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

June 17, 2025
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

June 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

June 17, 2025
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.