ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Ma'ana

Ranar 25 ga watan Mayu, rana ce ta “Ranar Afirka”, wato ranar tunawa da kafuwar Kungiyar Hadin Kan Afirka, wadda daga bisani ta zama Kungiyar Tarayyar Afirka ta AU. A jiya Litinin, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da daukacin jakadun kasashen Afirka da ke kasar Sin a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, inda suka gudanar da bikin murnar wannan rana mai ma’anar musamman ga Afirka. Wannan ya nuna abokantaka da ke tsakanin Sin da Afirka, tare da shaida yadda mutanen Sin da Afirka suke dora muhimmanci kan da’a.

‘Yan Afirka, kamar Sinawa, suna mai da hankali sosai ga da’a. A duk lokacin bukukuwa, na kan samu kiran waya da gaisuwa daga abokai ‘yan Afirka da yawa. Ina ganin za su iya fahimtar muhimmancin bikin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya shirya a wannan karo, da sauran abubuwan da suka nuna yadda jama’ar kasar Sin suke daukar da’a da muhimmanci, misalin ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin ya kan kai Afirka a farkon kowace shekara.

  • Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri
  • Tsarin Dunkulewar Aiki Ba Da Ilmi Da Kimiyya Da Kwararru Na Sin Ya Dace Da Yanayin Zamani

Da’a ba ta shafi “al’ada” kawai ba, tana kuma wakiltar ka’idoji da dabi’a, da dorewar huldar mutane da ta kasa da kasa. Kamar dai wannan biki na tunawa da “ranar Afirka”, wanda ya tattaro wakilan Sin da Afirka, don waiwayar yadda jama’ar Sin da ta Afirka suka nuna goyon baya ga juna a fafutukar kare ikon mulkin kasa, da kuma taimakawa juna a kokarin farfado da al’umma, tare da alkawarin ci gaba da kokarin hadin kai a nan gaba. Wannan yanayin hulda mai dorewa yana baiwa mutane damar mai da hankali kan tsare-tsaren ci gaba na dogon lokaci, da kuma neman inganta dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashe a kai a kai. Kasar da ke da da’a da mutunci ba za ta taba kaddamar da yakin haraji kan kasashen duniya ba, saboda ta fahimci darajar kwanciyar hankali da yanayin tabbaci ga ci gaban wata kasa da na al’ummarta cikin dogon lokaci.

ADVERTISEMENT

 

Da’a da dabi’a sun shafi mutunta juna, wanda shi ne abin da ake bukata don samun sakamako mai gamsarwa ga dukkan bangarorin da suke hadin gwiwa da juna. Saboda tana mutunta kasashen Afirka, kasar Sin ta iya daidaita yadda ake rarraba moriya a hadin gwiwar da ke tsakaninta da Afirka, da kuma ba da karin goyon baya wajen biyan bukatun raya kasashen Afirka. Misali, a shekarar 2024, kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga Afirka sun karu da kashi 6.9%, wanda ya zarta karuwar kashi 3.5% na kayayyakin da take fitarwa zuwa kasashen Afirka. Ban da haka, yankunan ciniki cikin ‘yanci na Lekki, da na Ogun-Guangdong da kamfanonin kasar Sin suka zuba jari a cikinsu, da gina su, da sarrafa su a Najeriya, sun samar da guraben ayyukan yi sama da 20,000 ga al’ummar Najeriya, tare da jawo jarin kimanin dalar Amurka biliyan 2.6. Wadannan misalan sun nuna irin kokarin da kasar Sin ke yi na inganta hadin gwiwa mai amfanar juna tare da kasashen Afirka. Ba kamar a wata kasa ta daban ba, inda aka tilastawa shugaban wata babbar kasa ta Afirka da ya yi hakuri da tsokana, da wulakanci a gaban daukacin jama’ar duniya baki daya. Irin wannan kasa bata ganin komai sai karfi kadai, tana son cin moriya da faduwar wani, kuma ba ta san da’a da mutunci, da yiwuwar samun ci gaba na bai daya ba.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

 

Tabbas a halin yanzu, wasu kasashe ba su ba da’a muhimmanci ba, kana suna ta daukar matakan kashin kai yadda suka ga dama, lamarin da ya sa al’amuran kasa da kasa suka shiga rudani. Dangane da wannan batu, dole ne Sin da kasashen Afirka masu da’a su karfafa hadin kai, su yi adawa da siyasar nuna fin karfi, da daukaka ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori masu fada-a-ji a duniya, da kare tsarin kasa da kasa dake karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya. Ta la’akari da yadda adadin yawan al’ummar Sin da Afirka ya kai kashi daya bisa uku na yawan al’ummar duniya, kokarin hadin gwiwarmu tabbas zai karkata duniya zuwa ga turba mai dacewa. (Bello Wang)

Ma'ana
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Ma'ana
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.