ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Ma'ana

Ranar 25 ga watan Mayu, rana ce ta “Ranar Afirka”, wato ranar tunawa da kafuwar Kungiyar Hadin Kan Afirka, wadda daga bisani ta zama Kungiyar Tarayyar Afirka ta AU. A jiya Litinin, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da daukacin jakadun kasashen Afirka da ke kasar Sin a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, inda suka gudanar da bikin murnar wannan rana mai ma’anar musamman ga Afirka. Wannan ya nuna abokantaka da ke tsakanin Sin da Afirka, tare da shaida yadda mutanen Sin da Afirka suke dora muhimmanci kan da’a.

‘Yan Afirka, kamar Sinawa, suna mai da hankali sosai ga da’a. A duk lokacin bukukuwa, na kan samu kiran waya da gaisuwa daga abokai ‘yan Afirka da yawa. Ina ganin za su iya fahimtar muhimmancin bikin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya shirya a wannan karo, da sauran abubuwan da suka nuna yadda jama’ar kasar Sin suke daukar da’a da muhimmanci, misalin ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin ya kan kai Afirka a farkon kowace shekara.

  • Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri
  • Tsarin Dunkulewar Aiki Ba Da Ilmi Da Kimiyya Da Kwararru Na Sin Ya Dace Da Yanayin Zamani

Da’a ba ta shafi “al’ada” kawai ba, tana kuma wakiltar ka’idoji da dabi’a, da dorewar huldar mutane da ta kasa da kasa. Kamar dai wannan biki na tunawa da “ranar Afirka”, wanda ya tattaro wakilan Sin da Afirka, don waiwayar yadda jama’ar Sin da ta Afirka suka nuna goyon baya ga juna a fafutukar kare ikon mulkin kasa, da kuma taimakawa juna a kokarin farfado da al’umma, tare da alkawarin ci gaba da kokarin hadin kai a nan gaba. Wannan yanayin hulda mai dorewa yana baiwa mutane damar mai da hankali kan tsare-tsaren ci gaba na dogon lokaci, da kuma neman inganta dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashe a kai a kai. Kasar da ke da da’a da mutunci ba za ta taba kaddamar da yakin haraji kan kasashen duniya ba, saboda ta fahimci darajar kwanciyar hankali da yanayin tabbaci ga ci gaban wata kasa da na al’ummarta cikin dogon lokaci.

ADVERTISEMENT

 

Da’a da dabi’a sun shafi mutunta juna, wanda shi ne abin da ake bukata don samun sakamako mai gamsarwa ga dukkan bangarorin da suke hadin gwiwa da juna. Saboda tana mutunta kasashen Afirka, kasar Sin ta iya daidaita yadda ake rarraba moriya a hadin gwiwar da ke tsakaninta da Afirka, da kuma ba da karin goyon baya wajen biyan bukatun raya kasashen Afirka. Misali, a shekarar 2024, kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga Afirka sun karu da kashi 6.9%, wanda ya zarta karuwar kashi 3.5% na kayayyakin da take fitarwa zuwa kasashen Afirka. Ban da haka, yankunan ciniki cikin ‘yanci na Lekki, da na Ogun-Guangdong da kamfanonin kasar Sin suka zuba jari a cikinsu, da gina su, da sarrafa su a Najeriya, sun samar da guraben ayyukan yi sama da 20,000 ga al’ummar Najeriya, tare da jawo jarin kimanin dalar Amurka biliyan 2.6. Wadannan misalan sun nuna irin kokarin da kasar Sin ke yi na inganta hadin gwiwa mai amfanar juna tare da kasashen Afirka. Ba kamar a wata kasa ta daban ba, inda aka tilastawa shugaban wata babbar kasa ta Afirka da ya yi hakuri da tsokana, da wulakanci a gaban daukacin jama’ar duniya baki daya. Irin wannan kasa bata ganin komai sai karfi kadai, tana son cin moriya da faduwar wani, kuma ba ta san da’a da mutunci, da yiwuwar samun ci gaba na bai daya ba.

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

 

Tabbas a halin yanzu, wasu kasashe ba su ba da’a muhimmanci ba, kana suna ta daukar matakan kashin kai yadda suka ga dama, lamarin da ya sa al’amuran kasa da kasa suka shiga rudani. Dangane da wannan batu, dole ne Sin da kasashen Afirka masu da’a su karfafa hadin kai, su yi adawa da siyasar nuna fin karfi, da daukaka ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori masu fada-a-ji a duniya, da kare tsarin kasa da kasa dake karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya. Ta la’akari da yadda adadin yawan al’ummar Sin da Afirka ya kai kashi daya bisa uku na yawan al’ummar duniya, kokarin hadin gwiwarmu tabbas zai karkata duniya zuwa ga turba mai dacewa. (Bello Wang)

Ma'ana
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
Ma'ana
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

LABARAI MASU NASABA

An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.