• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba

byAbubakar Sulaiman
6 months ago
Ribas

Kungiyar kwadago ta yi gargadin cewa za a iya tilasta mata daukar matakan da za su iya kawo cikas ga ayyukan tattalin arzikin kasa nan, wanda ta yi barazanar shiga yajin aiki matukar ba a janye dokar ta-ɓaci a da kakaba a Jihar Ribas cikin gaggawa.

kungiyar ta dai fitar da barazanar ce a cikin wata sanarwa da shugabanta na Jihar Ribas, Aled Agwanwor da shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta jihar, TUC, Ikechukwu Onyefuru da shugaban majalisar tattaunawa ta hadin gwiwa (JNC), Chuku Emecheta.

  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
  • Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi

kungiyoyin kwadago sun nuna damuwarsu game da shari’a da tasirin tattalin arziki da kuma ayyana dokar ta-ɓaci ta Shugaba Bola Tinubu ya kakaba a Jihar Ribas.

Sun bayyana cewa ayyana dokar ta-vaci da kuma dakatar da zavavven gwamna, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da mambobin majalisar jihar a matsayin wanda ya sava dokan kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Shugabannin kwadago sun dage cewa mutanen Jihar Ribas sun zavi wadannan jami’an ne cikin ‘yanci, kuma duk wani yunkuri na cire su da ya sava wa kundin tsarin mulki yana lalata dimokuraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

A cewar shugabannin Ƙwadago, dole ne a sauya irin wadannan lamari don kare mutuncin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya.

Sun jaddada wahalar da dokar ta-ɓaci ta haifar wa ma’aikatan kananan hukumomi, da yawa daga cikinsu har yanzu ba su karɓi albashinsu ba.

Sanarwar ta lura cewa hana albashin ma’aikata ya jefa su cikin matsin tattalin arziki, musamman ma a irin wannan lokaci da ake samun tsadar rayuwa a cikin kasar nan.

Ƙungiyar Ƙwadago ta yi gargadin cewa dokar ta-vaci na iya haifar da mummunan sakamako na tattalin arziki, tana mai jaddada muhimmancin da Jihar Ribas ke da ita ga tattalin arzikin Nijeriya da yankin Neja Delta gaba daya.

Ta ce da ma can kasar nan ta riga ta fuskanci hauhawar farashi, raguwar darajar naira, tsadar musayar canji, rashin aikin yi da tsadar rayuwa, rashin kwanciyar hankali a Jihar Ribas na iya kara ta’azzara halin da ake ciki a duk fadin kasar nan.

Sanarwar ta kuma nuna cewa rashin tabbas na siyasa da dokar ta-ɓaci ta haifar ya kori masu saka hannun jari wadanda suka nuna sha’awar zuba hannun jari a tattalin arzikin jihar.

“Wannan asarar saka hannun jari yana lalata kudaden shiga na cikin gida na jihar (IGR), kuma zai yi tasiri na dogon lokaci a ci gaban tattalin arziki da kuma damar samar da ayyukan yi a yankin.

“Duk da cewa mun amince da bukatar kiyaye doka da oda, dole ne a aiwatar da irin wadannan matakai a cikin tsarin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Dakatar da zaɓaɓɓun jami’ai da lalata tsarin biyan albashin ma’aikata ya keta hakkoki dan’adam wanda zai iya ta’azzara rashin tsaro da kalubalen tattalin arziki.

“Ya kamata gwamnatin tarayya ta ba da fifiko ga tsaro da jin dadin ‘yan kasa a kan muradun siyasa.

“Duk wata hanyar mulki da ke sadaukar da jin dadin ma’aikata don ayyukan siyasa zai kara tashin hankali da rashin kwanciyar hankali ga al’umma,” in ji ƙungiyar ƙwadago.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki

Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version