ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Ribas

Kungiyar kwadago ta yi gargadin cewa za a iya tilasta mata daukar matakan da za su iya kawo cikas ga ayyukan tattalin arzikin kasa nan, wanda ta yi barazanar shiga yajin aiki matukar ba a janye dokar ta-ɓaci a da kakaba a Jihar Ribas cikin gaggawa.

kungiyar ta dai fitar da barazanar ce a cikin wata sanarwa da shugabanta na Jihar Ribas, Aled Agwanwor da shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta jihar, TUC, Ikechukwu Onyefuru da shugaban majalisar tattaunawa ta hadin gwiwa (JNC), Chuku Emecheta.

  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
  • Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi

kungiyoyin kwadago sun nuna damuwarsu game da shari’a da tasirin tattalin arziki da kuma ayyana dokar ta-ɓaci ta Shugaba Bola Tinubu ya kakaba a Jihar Ribas.

ADVERTISEMENT

Sun bayyana cewa ayyana dokar ta-vaci da kuma dakatar da zavavven gwamna, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da mambobin majalisar jihar a matsayin wanda ya sava dokan kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Shugabannin kwadago sun dage cewa mutanen Jihar Ribas sun zavi wadannan jami’an ne cikin ‘yanci, kuma duk wani yunkuri na cire su da ya sava wa kundin tsarin mulki yana lalata dimokuraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

A cewar shugabannin Ƙwadago, dole ne a sauya irin wadannan lamari don kare mutuncin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya.

Sun jaddada wahalar da dokar ta-ɓaci ta haifar wa ma’aikatan kananan hukumomi, da yawa daga cikinsu har yanzu ba su karɓi albashinsu ba.

Sanarwar ta lura cewa hana albashin ma’aikata ya jefa su cikin matsin tattalin arziki, musamman ma a irin wannan lokaci da ake samun tsadar rayuwa a cikin kasar nan.

Ƙungiyar Ƙwadago ta yi gargadin cewa dokar ta-vaci na iya haifar da mummunan sakamako na tattalin arziki, tana mai jaddada muhimmancin da Jihar Ribas ke da ita ga tattalin arzikin Nijeriya da yankin Neja Delta gaba daya.

Ta ce da ma can kasar nan ta riga ta fuskanci hauhawar farashi, raguwar darajar naira, tsadar musayar canji, rashin aikin yi da tsadar rayuwa, rashin kwanciyar hankali a Jihar Ribas na iya kara ta’azzara halin da ake ciki a duk fadin kasar nan.

Sanarwar ta kuma nuna cewa rashin tabbas na siyasa da dokar ta-ɓaci ta haifar ya kori masu saka hannun jari wadanda suka nuna sha’awar zuba hannun jari a tattalin arzikin jihar.

“Wannan asarar saka hannun jari yana lalata kudaden shiga na cikin gida na jihar (IGR), kuma zai yi tasiri na dogon lokaci a ci gaban tattalin arziki da kuma damar samar da ayyukan yi a yankin.

“Duk da cewa mun amince da bukatar kiyaye doka da oda, dole ne a aiwatar da irin wadannan matakai a cikin tsarin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Dakatar da zaɓaɓɓun jami’ai da lalata tsarin biyan albashin ma’aikata ya keta hakkoki dan’adam wanda zai iya ta’azzara rashin tsaro da kalubalen tattalin arziki.

“Ya kamata gwamnatin tarayya ta ba da fifiko ga tsaro da jin dadin ‘yan kasa a kan muradun siyasa.

“Duk wata hanyar mulki da ke sadaukar da jin dadin ma’aikata don ayyukan siyasa zai kara tashin hankali da rashin kwanciyar hankali ga al’umma,” in ji ƙungiyar ƙwadago.

 

Ribas
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki

Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.