ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Cikin Gidan Jam’iyyar NNPP Na Kara Rincabewa A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
NNPP

A yayin da ya rage ‘yan kwanaki kotun koli ta yanke hukunci kan daukaka karar da Gwamnan Kano tare da Jam’iyyarsa NNPP suka yi, wanda suke kalubalantar hukuncin kotun sararon korafe-korafen zabe da kuma hukuncin da kotun daukaka kara suka zartar. Duka kotunan guda biyu sun bayyana Dakta Nasiru Yusuf Gawuna a matsyain halastaccen zababben Gwamnan Kano.

Yanzu haka dai lamarin na sake daukar sabon salo bayan yadda jam’iyyar NNPP da magoya bayanta suka rungumi tsarin addu’o’in samun nasara a kotun koli, bayan wani lokoci kuma suka shagala da batun zanga-zangar da suke toshe hanyoyin shigowa Kano da kuma yin sallar alkunuti.

  • Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika – NNPP
  • Zaben 2023: NNPP Ta Ci Zabe Ta Hanyar Magudi A Kano – Doguwa

Cikin makon da ya gabata, an wayi gari da kiraye-kiranyen zanga-zangar mata wadda hakan ya sa malamai suka fara tofa albarkacin bakinsu kan illar da ke tattare da umarnin fitowar mata zanga-zanga.

ADVERTISEMENT

Babban limamin Masallachin Juma’a Na Triump wanda ya bayyana rashin da cewa fitowar matan musulmi zanga-zangar siyasa. Ya tambayi masu shirya zanga-zangar matan da cewa mai ya sa ba a ga matar gwamna da sauran matan mahukuntan gwamnatin ba.

A cikin abubuwan da ake kallo a matsayin sabon rikicin cikin gidan jam’iyyar ta NNPP, wata majiya da ta bukaci a sakaya sunanta ta shaida cewa, gwamnatin Kano ta kori ma’aikata sama da dubu goma sha biyu wadanda gwamnatin baya ta dauka aiki.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Majiyar ta ce sakamakon rushe-rushe da gwamnati ta aiwatar ya haifar da mummunan bakin jini ga gwamnatin.
Ba a jima da fitar da wannan sanarwa ba sai gwamnatin ta sauya shawara, inda aka yi wa ma’aikatan fuskar shanu tare da kin dawo da su tsarin biyan albashin, abin da ya sa wani jami’in gwmanatin ya matsa lamba wajen shawartar gwamna domin cika wancan alkawari, wanda majiyar ta shaida cewa wannan kokarin tuna wa gwamna wancan alkawari ne ya haifar da wata gagarumar matsalar da a halin yanzu wasu hotuna ke ta yawo a kafafen sada zumunta, inda ake nuna wasu manyan jami’an gwamnati na musayar yawu tare da alkawarin za a saki cikakken faifan bidoiyon.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
ta'addanci

Wasu Manyan Kasa Ke Daukar Nauyin Ta’addanci – Ministan Ma’adanai

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.