• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

by Sulaiman
3 months ago
Abuja

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Rikicin da ya barke tsakanin Fulani da Gwarawa a kauyen Gurfata da ke karamar hukumar Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ya yi sanadin mutuwar mutum daya tare da raunata wasu da dama, yayin da wasu da dama suka rasa muhallansu bayan da aka kona gidaje 31.
Lamarin wanda ya afku a ranar Talatar da ta gabata, rahotanni sun ce ya samo asali ne daga takaddamar hanya da ta bi ta cikin gonar wani manomi gwari mai suna Sa’adu wacce wani Bafulatani makiyayi mai suna Shaibu Adamu ya yi yunkurin bi da shanunsa ta kan wannan hanya.
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
Mai sharhi kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya bayar da cikakken rahoto game da rikicin a wani bayani da ya wallafa a shafinsa na X (Twitter) a ranar Laraba.
A cewar Makama, rikicin ya fara ne a lokacin da Adamu ya yi yunkurin ratsa gonar Sa’adu, amma manomin ya ki amincewa, inda ya dage sai dai ya bi ta wata hanya ta daban.
Makama ya ce rashin jituwar da ke tsakanin mutanen biyu ta kai ga doke-doke.
“Nan da nan, al’amura suka kara kazanta yayin da dan uwan makiyayi Shaibu, Adamu Ibrahim, ya kai wa wani manomi dan garin hari, Dahiru Yakubu, da adda.
“An garzaya da Yakubu zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abuja, inda daga baya ya rasu,” In ji Makama.
Labarin mutuwar Yakubu ya haifar da harin ramuwar gayya daga fusatattun matasan Gwari, inda suka far wa Fulani a kauyen, inda suka kona gidaje 31 tare da raunata akalla mutane uku.
Daga baya an tura sojoji tare da wasu jami’an tsaro zuwa yankin domin kwantar da tarzoma da kuma dawo da zaman lafiya.
“Hukumomi sun yi kira da a samar da zaman lafiya tare da yin kira ga al’ummomin biyu da su yi hakuri, a halin da ake ciki, ana ci gaba da kokarin sasanta bangarorin biyu da kuma hana barkewar rikici.”
Ya kara da cewa har zuwa yau Laraba al’amura sun koma kamar yadda aka saba duk da cewa har yanzu ana zaman dar-dar.
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Next Post
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.