ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

by Sulaiman
11 months ago
Abuja

LABARAI MASU NASABA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Rikicin da ya barke tsakanin Fulani da Gwarawa a kauyen Gurfata da ke karamar hukumar Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ya yi sanadin mutuwar mutum daya tare da raunata wasu da dama, yayin da wasu da dama suka rasa muhallansu bayan da aka kona gidaje 31.
Lamarin wanda ya afku a ranar Talatar da ta gabata, rahotanni sun ce ya samo asali ne daga takaddamar hanya da ta bi ta cikin gonar wani manomi gwari mai suna Sa’adu wacce wani Bafulatani makiyayi mai suna Shaibu Adamu ya yi yunkurin bi da shanunsa ta kan wannan hanya.
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
Mai sharhi kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya bayar da cikakken rahoto game da rikicin a wani bayani da ya wallafa a shafinsa na X (Twitter) a ranar Laraba.
A cewar Makama, rikicin ya fara ne a lokacin da Adamu ya yi yunkurin ratsa gonar Sa’adu, amma manomin ya ki amincewa, inda ya dage sai dai ya bi ta wata hanya ta daban.
Makama ya ce rashin jituwar da ke tsakanin mutanen biyu ta kai ga doke-doke.
“Nan da nan, al’amura suka kara kazanta yayin da dan uwan makiyayi Shaibu, Adamu Ibrahim, ya kai wa wani manomi dan garin hari, Dahiru Yakubu, da adda.
“An garzaya da Yakubu zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abuja, inda daga baya ya rasu,” In ji Makama.
Labarin mutuwar Yakubu ya haifar da harin ramuwar gayya daga fusatattun matasan Gwari, inda suka far wa Fulani a kauyen, inda suka kona gidaje 31 tare da raunata akalla mutane uku.
Daga baya an tura sojoji tare da wasu jami’an tsaro zuwa yankin domin kwantar da tarzoma da kuma dawo da zaman lafiya.
“Hukumomi sun yi kira da a samar da zaman lafiya tare da yin kira ga al’ummomin biyu da su yi hakuri, a halin da ake ciki, ana ci gaba da kokarin sasanta bangarorin biyu da kuma hana barkewar rikici.”
Ya kara da cewa har zuwa yau Laraba al’amura sun koma kamar yadda aka saba duk da cewa har yanzu ana zaman dar-dar.
Abuja
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Sulaiman
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
Rahotonni

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Rahotonni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Next Post
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

LABARAI MASU NASABA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.