• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

by Rabi'u Ali Indabawa
9 seconds ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rikicin Masarautar Kano ya dauki wani salo na daban, yayin da Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya ce magoya bayansa sun yi kokarin kare kansu ne a rikicin da ya barke a ranar Lahadi a fadar Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II.

A ranar Lahadin da ta gabata ce magoya bayan Sarki Sanusi II da na Sarkin Bayero suka yi artabu a fadar Sarki Sanusi na Kofar Kudu, lamarin da gwamnatin jihar ta bayyana a matsayin abin takaici, inda ta bayyana cewa an jikkata wasu ‘yan jihar da ba su ji ba ba su gani ba.

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

A wata sanarwa da sashen yada labaran Masarautar Kano ta fitar tun farko mai dauke da sa hannun Sadam Yakasai, ta ce Sarki Sanusi yana wajen fadar a lokacin da lamarin ya faru.

Ya ce, “Sun fasa kofar ne suka far wa masu gadin, inda suka jikkata wasu daga cikinsu, suka farfasa motocin ‘yansandan da ke cikin fadar, da gangan Aminu ya bi ta hanyar fadar sarki maimakon ya bi hanyar da ta dace daga Koki zuwa Nassarawa, sai ‘yan bindigar suka yanke shawarar kai hari Gidan Rumfa.”

Sai dai da yake mayar da martani kan lamarin na ranar Lahadi, Sarki Ado Bayero ya ce a jiya magoya bayansa sun yi hakan ne domin kare kansu.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Mai taimaka wa Sarkin Bayero kan harkokin yada labarai, Khalid Uba, ya shaida wa LEADERSHIP cewa magoya bayan Sarkin Bayero ba su da makamai.

Uba, wanda ya zanta da wakilinmu ta wayar tarho, ya ci gaba da cewa babu wani daga cikin tawagar Sarkin Bayero da ke dauke da wani makami, sai dai an tilasta musu dakile harin.

A cewarsa, wannan ba shi ne karo na farko da Sarkin Bayero ya taba bi ta wannan hanyar ba.

“Bayan isowarmu daga gidan Dantata domin jaje, wasu matasa sun mamaye titin da duwatsu da makamai a Kofar Kudu.

“Lokacin da muka isa Kofar Kudu, sai suka fara jifan mu, amma aka yi sa’a, mun yi nasarar fatattakar su zuwa cikin gida, kuma Sarkin ya wuce cikin nasara ba tare da wani ya samu rauni ba,” in ji shi.

Uba ya tabbatar da korar magoya bayan Sarkin Bayero daga fadar, inda ya ce sun samu korafe-korafe daban-daban a kan lamarin.

 

Sarakuna biyu a gari daya

Rikici ya barke a Masarautar Kano biyo bayan matakin da gwamnatin jihar ta dauka na mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano na 16.

Maido da masarautun ya biyo bayan sake duba dokar Masarautar da ta samar da karin masarautu guda hudu.

An dai kalubalanci matakin a gaban kotu, inda Aminu Ado Bayero ya ki amincewa ya yi murabus daga karagar mulki. Ya ci gaba da zama fadar Nasarawa a karkashin kulawar jami’an tsaro.

A ranar 23 ga Mayu, 2024, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya mayar da Sanusi Sarkin Kano. Tun shekaru hudu da suka gabata ne tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya tsige Sanusi daga mukamin sarki, wanda ya jagoranci masarautar Kano da kuma tsige Sanusi daga karagar mulki.

 

Wadanda aka kora daga fadar sun koka da makomarsu

A halin da ake ciki, daya daga cikin wadanda aka kora daga fadar, wacce ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya jefa ta da ’yan uwanta cikin rudani inda aka tilasta musu barin fadar.

Ta yi zargin cewa mutanen da suka fatattake su sun fito ne da ‘yan daba, inda suka cire rufin kofofi da tagoginsu, suka kuma umarce su da su bar fadar cikin sa’o’i 24.

Ta kara da cewa mutanen sun zazzagi wadanda ba su son Sarki Sanusi ko kuma masu biyayya ga Sarki Bayero tare da yin barazanar cutar da duk wanda ya ki amincewa da korarsu.

“Wasu mutanen da ke Kofar Kwaru an riga an ba su sanarwar a ranar Lahadi da tsakar dare don su fice ranar Litinin, yayin da mutane irin mu suka shiga halin rashin tabbas a ranar Litinin.

“An dauki matakin ‘yansanda kafin su ba mu damar kwana har zuwa yau (Talata), amma a halin yanzu, mun yi tattara kayanmu domin komawa ga wasu ‘yan uwa,” in ji ta.

Ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta shiga tsakani, inda ta koka da rashin taimakon su.

A halin da ake ciki, rundunar ‘yansandan Jihar Kano ta ce ta kama wasu mutum hudu da ake zargi da hannu a harin da aka kai a fadar Sarki Sanusi da ke Kofar Kudu a cikin birnin Kano ranar Lahadi.

Hakan ya biyo bayan wata arangama da aka yi tsakanin magoya bayan Sarkin Kano na 16, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, da magoya bayan Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, a fadar Sarki Sanusi na Kofar Kudu.

Kakakin rundunar SP Abdullahi Kiyawa ya shaida wa manema labarai a Kano cewa wadanda ake zargin suna hannun ‘yansanda kuma suna kan bincike.

A cewarsa, kwamishinan ‘yansandan jihar, Ibrahim Bakori, ya kafa kwamitin da zai binciki fadan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoMasarautaRikici
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Related

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

1 hour ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

11 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

20 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

22 hours ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

1 day ago
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara
Manyan Labarai

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

1 day ago

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.