• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rikicin Masarautar Kano ya dauki wani salo na daban, yayin da Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya ce magoya bayansa sun yi kokarin kare kansu ne a rikicin da ya barke a ranar Lahadi a fadar Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II.

A ranar Lahadin da ta gabata ce magoya bayan Sarki Sanusi II da na Sarkin Bayero suka yi artabu a fadar Sarki Sanusi na Kofar Kudu, lamarin da gwamnatin jihar ta bayyana a matsayin abin takaici, inda ta bayyana cewa an jikkata wasu ‘yan jihar da ba su ji ba ba su gani ba.

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

A wata sanarwa da sashen yada labaran Masarautar Kano ta fitar tun farko mai dauke da sa hannun Sadam Yakasai, ta ce Sarki Sanusi yana wajen fadar a lokacin da lamarin ya faru.

Ya ce, “Sun fasa kofar ne suka far wa masu gadin, inda suka jikkata wasu daga cikinsu, suka farfasa motocin ‘yansandan da ke cikin fadar, da gangan Aminu ya bi ta hanyar fadar sarki maimakon ya bi hanyar da ta dace daga Koki zuwa Nassarawa, sai ‘yan bindigar suka yanke shawarar kai hari Gidan Rumfa.”

Sai dai da yake mayar da martani kan lamarin na ranar Lahadi, Sarki Ado Bayero ya ce a jiya magoya bayansa sun yi hakan ne domin kare kansu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

Mai taimaka wa Sarkin Bayero kan harkokin yada labarai, Khalid Uba, ya shaida wa LEADERSHIP cewa magoya bayan Sarkin Bayero ba su da makamai.

Uba, wanda ya zanta da wakilinmu ta wayar tarho, ya ci gaba da cewa babu wani daga cikin tawagar Sarkin Bayero da ke dauke da wani makami, sai dai an tilasta musu dakile harin.

A cewarsa, wannan ba shi ne karo na farko da Sarkin Bayero ya taba bi ta wannan hanyar ba.

“Bayan isowarmu daga gidan Dantata domin jaje, wasu matasa sun mamaye titin da duwatsu da makamai a Kofar Kudu.

“Lokacin da muka isa Kofar Kudu, sai suka fara jifan mu, amma aka yi sa’a, mun yi nasarar fatattakar su zuwa cikin gida, kuma Sarkin ya wuce cikin nasara ba tare da wani ya samu rauni ba,” in ji shi.

Uba ya tabbatar da korar magoya bayan Sarkin Bayero daga fadar, inda ya ce sun samu korafe-korafe daban-daban a kan lamarin.

 

Sarakuna biyu a gari daya

Rikici ya barke a Masarautar Kano biyo bayan matakin da gwamnatin jihar ta dauka na mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano na 16.

Maido da masarautun ya biyo bayan sake duba dokar Masarautar da ta samar da karin masarautu guda hudu.

An dai kalubalanci matakin a gaban kotu, inda Aminu Ado Bayero ya ki amincewa ya yi murabus daga karagar mulki. Ya ci gaba da zama fadar Nasarawa a karkashin kulawar jami’an tsaro.

A ranar 23 ga Mayu, 2024, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya mayar da Sanusi Sarkin Kano. Tun shekaru hudu da suka gabata ne tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya tsige Sanusi daga mukamin sarki, wanda ya jagoranci masarautar Kano da kuma tsige Sanusi daga karagar mulki.

 

Wadanda aka kora daga fadar sun koka da makomarsu

A halin da ake ciki, daya daga cikin wadanda aka kora daga fadar, wacce ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya jefa ta da ’yan uwanta cikin rudani inda aka tilasta musu barin fadar.

Ta yi zargin cewa mutanen da suka fatattake su sun fito ne da ‘yan daba, inda suka cire rufin kofofi da tagoginsu, suka kuma umarce su da su bar fadar cikin sa’o’i 24.

Ta kara da cewa mutanen sun zazzagi wadanda ba su son Sarki Sanusi ko kuma masu biyayya ga Sarki Bayero tare da yin barazanar cutar da duk wanda ya ki amincewa da korarsu.

“Wasu mutanen da ke Kofar Kwaru an riga an ba su sanarwar a ranar Lahadi da tsakar dare don su fice ranar Litinin, yayin da mutane irin mu suka shiga halin rashin tabbas a ranar Litinin.

“An dauki matakin ‘yansanda kafin su ba mu damar kwana har zuwa yau (Talata), amma a halin yanzu, mun yi tattara kayanmu domin komawa ga wasu ‘yan uwa,” in ji ta.

Ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta shiga tsakani, inda ta koka da rashin taimakon su.

A halin da ake ciki, rundunar ‘yansandan Jihar Kano ta ce ta kama wasu mutum hudu da ake zargi da hannu a harin da aka kai a fadar Sarki Sanusi da ke Kofar Kudu a cikin birnin Kano ranar Lahadi.

Hakan ya biyo bayan wata arangama da aka yi tsakanin magoya bayan Sarkin Kano na 16, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, da magoya bayan Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, a fadar Sarki Sanusi na Kofar Kudu.

Kakakin rundunar SP Abdullahi Kiyawa ya shaida wa manema labarai a Kano cewa wadanda ake zargin suna hannun ‘yansanda kuma suna kan bincike.

A cewarsa, kwamishinan ‘yansandan jihar, Ibrahim Bakori, ya kafa kwamitin da zai binciki fadan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoMasarautaRikici
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Next Post

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

Related

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

16 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

23 hours ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

23 hours ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

1 day ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

1 day ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

2 days ago
Next Post
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

LABARAI MASU NASABA

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.