ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Kano

Rikicin Masarautar Kano ya dauki wani salo na daban, yayin da Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya ce magoya bayansa sun yi kokarin kare kansu ne a rikicin da ya barke a ranar Lahadi a fadar Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II.

A ranar Lahadin da ta gabata ce magoya bayan Sarki Sanusi II da na Sarkin Bayero suka yi artabu a fadar Sarki Sanusi na Kofar Kudu, lamarin da gwamnatin jihar ta bayyana a matsayin abin takaici, inda ta bayyana cewa an jikkata wasu ‘yan jihar da ba su ji ba ba su gani ba.

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

A wata sanarwa da sashen yada labaran Masarautar Kano ta fitar tun farko mai dauke da sa hannun Sadam Yakasai, ta ce Sarki Sanusi yana wajen fadar a lokacin da lamarin ya faru.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Sun fasa kofar ne suka far wa masu gadin, inda suka jikkata wasu daga cikinsu, suka farfasa motocin ‘yansandan da ke cikin fadar, da gangan Aminu ya bi ta hanyar fadar sarki maimakon ya bi hanyar da ta dace daga Koki zuwa Nassarawa, sai ‘yan bindigar suka yanke shawarar kai hari Gidan Rumfa.”

Sai dai da yake mayar da martani kan lamarin na ranar Lahadi, Sarki Ado Bayero ya ce a jiya magoya bayansa sun yi hakan ne domin kare kansu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Mai taimaka wa Sarkin Bayero kan harkokin yada labarai, Khalid Uba, ya shaida wa LEADERSHIP cewa magoya bayan Sarkin Bayero ba su da makamai.

Uba, wanda ya zanta da wakilinmu ta wayar tarho, ya ci gaba da cewa babu wani daga cikin tawagar Sarkin Bayero da ke dauke da wani makami, sai dai an tilasta musu dakile harin.

A cewarsa, wannan ba shi ne karo na farko da Sarkin Bayero ya taba bi ta wannan hanyar ba.

“Bayan isowarmu daga gidan Dantata domin jaje, wasu matasa sun mamaye titin da duwatsu da makamai a Kofar Kudu.

“Lokacin da muka isa Kofar Kudu, sai suka fara jifan mu, amma aka yi sa’a, mun yi nasarar fatattakar su zuwa cikin gida, kuma Sarkin ya wuce cikin nasara ba tare da wani ya samu rauni ba,” in ji shi.

Uba ya tabbatar da korar magoya bayan Sarkin Bayero daga fadar, inda ya ce sun samu korafe-korafe daban-daban a kan lamarin.

 

Sarakuna biyu a gari daya

Rikici ya barke a Masarautar Kano biyo bayan matakin da gwamnatin jihar ta dauka na mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano na 16.

Maido da masarautun ya biyo bayan sake duba dokar Masarautar da ta samar da karin masarautu guda hudu.

An dai kalubalanci matakin a gaban kotu, inda Aminu Ado Bayero ya ki amincewa ya yi murabus daga karagar mulki. Ya ci gaba da zama fadar Nasarawa a karkashin kulawar jami’an tsaro.

A ranar 23 ga Mayu, 2024, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya mayar da Sanusi Sarkin Kano. Tun shekaru hudu da suka gabata ne tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya tsige Sanusi daga mukamin sarki, wanda ya jagoranci masarautar Kano da kuma tsige Sanusi daga karagar mulki.

 

Wadanda aka kora daga fadar sun koka da makomarsu

A halin da ake ciki, daya daga cikin wadanda aka kora daga fadar, wacce ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya jefa ta da ’yan uwanta cikin rudani inda aka tilasta musu barin fadar.

Ta yi zargin cewa mutanen da suka fatattake su sun fito ne da ‘yan daba, inda suka cire rufin kofofi da tagoginsu, suka kuma umarce su da su bar fadar cikin sa’o’i 24.

Ta kara da cewa mutanen sun zazzagi wadanda ba su son Sarki Sanusi ko kuma masu biyayya ga Sarki Bayero tare da yin barazanar cutar da duk wanda ya ki amincewa da korarsu.

“Wasu mutanen da ke Kofar Kwaru an riga an ba su sanarwar a ranar Lahadi da tsakar dare don su fice ranar Litinin, yayin da mutane irin mu suka shiga halin rashin tabbas a ranar Litinin.

“An dauki matakin ‘yansanda kafin su ba mu damar kwana har zuwa yau (Talata), amma a halin yanzu, mun yi tattara kayanmu domin komawa ga wasu ‘yan uwa,” in ji ta.

Ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta shiga tsakani, inda ta koka da rashin taimakon su.

A halin da ake ciki, rundunar ‘yansandan Jihar Kano ta ce ta kama wasu mutum hudu da ake zargi da hannu a harin da aka kai a fadar Sarki Sanusi da ke Kofar Kudu a cikin birnin Kano ranar Lahadi.

Hakan ya biyo bayan wata arangama da aka yi tsakanin magoya bayan Sarkin Kano na 16, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, da magoya bayan Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, a fadar Sarki Sanusi na Kofar Kudu.

Kakakin rundunar SP Abdullahi Kiyawa ya shaida wa manema labarai a Kano cewa wadanda ake zargin suna hannun ‘yansanda kuma suna kan bincike.

A cewarsa, kwamishinan ‘yansandan jihar, Ibrahim Bakori, ya kafa kwamitin da zai binciki fadan.

Kano
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.