• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
Sarauta

Kallo ya sake komawa kotu dangane da rikicin sarautar Kano, yayin da aka ci gaba da saurarar karar da aka shigar kan rushe masarautu da tsige sarakunansu.

A bangaren Sarki Muhammadu Sanusi II, wanda yake da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano ya ci gaba da shimfida mulki daga fadar gidan Dabo, inda yake samun kariyar gwamna da jami’an Karota, ‘yan tauri da jami’an sa-kai.

Yayin da Sarkin Aminu Ado Bayero ke zaman tasa fadar a gidan sarki na Nasarawa, wanda shi kuma ake hangen jami’an tsaron soja da ‘yansanda ke tsaronsa.

Tun bayan sake dawowar Sarki Muhammadu Sanusi II, sarkin ya fara limancin sallar Juma’a, sarkin ya yi sallah a masallacin Juma’a da ke fadar Gwmnatin Jihar Kano a makon farko bayan dawowarsa, haka zalika a makon da ya gabata ya jagoranci sallar juma’ar a babban masallacin sarki na Kano.

Abin da ke ci gaba da kai komo a zukatan Kanawa shi ne, yadda kotuna uku suka bayar da umarni daban-daban kan al’amarin. Inda kotun farko wadda babbar kotun tarayya ce da ke zamanta a Kano ta bayar da umarnin korar Sarki Muhammadu Sanusi II daga fadar gidan Rumfa.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

Kotun ta kuma umarci ‘yansanda da su tabbatar an ba Sarkin Kano na 15, Aminu Bayero duk wani hakki da alfarmar da ta kamata a ba shi.

Mai shari’a S. A. Amobeda wanda ya bayar da wannan umarnin ya bayyana cewa an yi wannan hukunci ne domin tabbatar da adalci da kuma wanzar da zaman lafiya a Jihar Kano.

Sai dai kuma wata kotun daban ta hana jami’an tsaro korar Sarki Sanusi II, sakamakon umarnin da Mai Shari’a, Amina Adamu Aliyu ta babbar. Kotun Kano da ke zamanta a titin Miller, ta hana ‘yansanda, hukumar tsaro ta farin kaya (SSS) da sojoji korar Sarki Sanusi II daga fada.

Sarki Sanusi II ne ya shigar da karar tare da masu nadin sarkin Kano hudu, wanda suka hada da Madakin Kano, Yusuf Nabahani da Makaman Kano, Ibrahim Sarki Abdullahi da Sarkin Bai, Mansur Adnan da Sarkin Dawaki Maituta, Bello Tuta.
Wannan hukunce-hukunci ta kara dagula lamura tsakanin Sarki Sanusi II da Aminu Bayero wadanda suke fafatawa a neman kujerar sarautar Kano. Rigimar dai ta janyo zanga-zangar a tsakanin magoya bayansu a sassan Jihar Kano.

Sai dai kuma sakamakon yajina kungiyar kwadago ta tsunduma ranar Litinin da ta gabata, wadda ita ce ranar da ake sa ran fara sauraron waccan kara ya sa dole an dage sauraron karar har zuwa ranar Alhamis.

A wani kokarin na kamo bakin zaren, Alkalin-alkalan Nijeriya ya kira manyan alkalan Kotun Tarayya da ke Jihar Kano kan bayar da hukunci masu cin karo da juna, domin warware dambarwar Masarautar Kano.

Sai dai duk wancan umarnin na kotu, an hangi akalla hakimai 40 suka yi mubayi’a ga mai martaba Sarkin Sanusi II.

Kano dai na da hakimai 65, wanda mubayi’ar 40 ga Sarkin Kano Sanusi II na nufin ya samu rinjaye goyon bayan hakiman kan wadanda suka goyi bayan Aminu Ado Bayero. Sai dai Bahaushe na cewa, ‘ba a san maci tuwo ba, sai miya ta kare.’

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na’urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na'urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.