• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kallo ya sake komawa kotu dangane da rikicin sarautar Kano, yayin da aka ci gaba da saurarar karar da aka shigar kan rushe masarautu da tsige sarakunansu.

A bangaren Sarki Muhammadu Sanusi II, wanda yake da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano ya ci gaba da shimfida mulki daga fadar gidan Dabo, inda yake samun kariyar gwamna da jami’an Karota, ‘yan tauri da jami’an sa-kai.

Yayin da Sarkin Aminu Ado Bayero ke zaman tasa fadar a gidan sarki na Nasarawa, wanda shi kuma ake hangen jami’an tsaron soja da ‘yansanda ke tsaronsa.

Tun bayan sake dawowar Sarki Muhammadu Sanusi II, sarkin ya fara limancin sallar Juma’a, sarkin ya yi sallah a masallacin Juma’a da ke fadar Gwmnatin Jihar Kano a makon farko bayan dawowarsa, haka zalika a makon da ya gabata ya jagoranci sallar juma’ar a babban masallacin sarki na Kano.

Abin da ke ci gaba da kai komo a zukatan Kanawa shi ne, yadda kotuna uku suka bayar da umarni daban-daban kan al’amarin. Inda kotun farko wadda babbar kotun tarayya ce da ke zamanta a Kano ta bayar da umarnin korar Sarki Muhammadu Sanusi II daga fadar gidan Rumfa.

Labarai Masu Nasaba

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun ta kuma umarci ‘yansanda da su tabbatar an ba Sarkin Kano na 15, Aminu Bayero duk wani hakki da alfarmar da ta kamata a ba shi.

Mai shari’a S. A. Amobeda wanda ya bayar da wannan umarnin ya bayyana cewa an yi wannan hukunci ne domin tabbatar da adalci da kuma wanzar da zaman lafiya a Jihar Kano.

Sai dai kuma wata kotun daban ta hana jami’an tsaro korar Sarki Sanusi II, sakamakon umarnin da Mai Shari’a, Amina Adamu Aliyu ta babbar. Kotun Kano da ke zamanta a titin Miller, ta hana ‘yansanda, hukumar tsaro ta farin kaya (SSS) da sojoji korar Sarki Sanusi II daga fada.

Sarki Sanusi II ne ya shigar da karar tare da masu nadin sarkin Kano hudu, wanda suka hada da Madakin Kano, Yusuf Nabahani da Makaman Kano, Ibrahim Sarki Abdullahi da Sarkin Bai, Mansur Adnan da Sarkin Dawaki Maituta, Bello Tuta.
Wannan hukunce-hukunci ta kara dagula lamura tsakanin Sarki Sanusi II da Aminu Bayero wadanda suke fafatawa a neman kujerar sarautar Kano. Rigimar dai ta janyo zanga-zangar a tsakanin magoya bayansu a sassan Jihar Kano.

Sai dai kuma sakamakon yajina kungiyar kwadago ta tsunduma ranar Litinin da ta gabata, wadda ita ce ranar da ake sa ran fara sauraron waccan kara ya sa dole an dage sauraron karar har zuwa ranar Alhamis.

A wani kokarin na kamo bakin zaren, Alkalin-alkalan Nijeriya ya kira manyan alkalan Kotun Tarayya da ke Jihar Kano kan bayar da hukunci masu cin karo da juna, domin warware dambarwar Masarautar Kano.

Sai dai duk wancan umarnin na kotu, an hangi akalla hakimai 40 suka yi mubayi’a ga mai martaba Sarkin Sanusi II.

Kano dai na da hakimai 65, wanda mubayi’ar 40 ga Sarkin Kano Sanusi II na nufin ya samu rinjaye goyon bayan hakiman kan wadanda suka goyi bayan Aminu Ado Bayero. Sai dai Bahaushe na cewa, ‘ba a san maci tuwo ba, sai miya ta kare.’


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aminu Ado BayerokanoMasarautar KanoSunusi Lamido Sanusi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na’urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

Related

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

31 minutes ago
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

11 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

13 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

15 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

15 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

18 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na’urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na'urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.