ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na’urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
Tarayya

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da na’urar auna masu kallo domin samar da sahihin bayanai na masu kallon talabijin a ƙasar nan.

A cikin wata sanarwa da Rabiu Ibrahim, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Ministan, Idris, wanda ya ƙaddamar da taron a Abuja a ranar Alhamis, ya ce na’urar tana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da cewa ayyukan watsa shirye-shirye ba wai kawai suna da tasiri ba har ma suna nuna abubuwa daban-daban da masu sauraro suka fi so kuma suke buƙata.

  • Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu
  • Kamfanin Google Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Darasi 10 Kan Kirkirarriyar Basira

Ya ce: “Kayan aiki ne wanda ke ba mu ikon fahimta da kuma ba da amsa ga yanayin masu amfani da kafofin watsa labarai, samar da kyakkyawar fahimta a cikin halayen kallon su, da abubuwan da suka fi so.

ADVERTISEMENT

“Don haka abin farin ciki ne a lura cewa a ƙarshe an samu nasara a wannan aikin da aka fara a shekarar 2020.”

Ministan ya bayyana ɓullo da na’urar a matsayin wani gagarumin cigaba da ya yi daidai da manufar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ganin Nijeriya ta samu cigaba da bunƙasar fasaha.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya ce ɓullo da na’urar ya zama dole sosai domin har yanzu Ma’aunin Masu Kallo ko Sauraro na yin amfani da tsohon tsarin Alƙalamin da Takarda na tattara bayanai kan masu kallon talabijin da masu sauraren rediyo, wanda hakan ba ya nuna haƙiƙanin abin da ko yawan mutanen da ke kallo ko sauraron wani shiri na musamman.

“Hakazalika, masu tashoshi, masu shirye-shirye, ‘yan wasa, ba su amfana ta hanyoyi da yawa; mafi muhimmanci, ba su da ƙwazo ko ƙalubalen samar da ƙarin shirye-shirye mafi kyau wanda ke biyan ‘buƙatu’, a matsayin ma’aunin wanda yake so, abin da yake so, yawan yadda yake so, da dai sauran su. Wannan ya hana ci gaban ɗaukacin harkokin nishaɗi da yaɗa labarai a Nijeriya.”

Ministan ya ce abin takaici ne ganin cewa duk da cewa ƙasar tana da yawan masu kallo sama da sau uku a Afirka ta Kudu, kuɗaɗen da ake samu a tallace-tallacen talabijin na Nijeriya ya yi kaɗan idan aka kwatanta shi da na ƙasar Afirka ta Kudu, da kuma Kenya, lamarin da ya sa dole a yi amfani da tsarin da zai tabbatar da cewa kuɗin da ake kashewa a tallace-tallace a Nijeriya ya ƙaru sosai cikin shekaru biyu masu zuwa.

Idris ya ce: “Ina da yaƙinin cewa Na’urar Auna Masu Sauraro na gaskiya kuma tabbatacce zai jawo hannun jari mai yawa a ɓangaren yaɗa labarai, da bunƙasa tattalin arziki da samar da ayyukan yi.

“Hakan kuma zai ƙara wa Nijeriya suna a matsayin kasuwa mai ingantacciyar hanyar nazarin kafafen yaɗa labarai.”

Idris ya ce aikin wanda zai samar da ayyukan yi 500 kai-tsaye da kuma ayyuka 2,500 a fakaice an tsara shi ne don da sake farfaɗo da harkar yaɗa labarai a Nijeriya da kuma inganta shi domin tunkarar zamani domin har yanzu Gwamnatin Tarayya na kan hanyar aiwatar da Canji zuwa Dijital.

Ya nanata ƙudirin Shugaba Tinubu na bunƙasa harkar yaɗa labarai gaba ɗaya a Nijeriya kamar yadda ya bayyana a cikin umarnin da ya ba Ma’aikatar Masana’antu, Kasuwanci da Saka Hannun Jari ta Tarayya da Bankin Masana’antu a kwanan baya na faɗaɗa hanyoyin hada-hadar kuɗi ga Masana’antar Watsa Labarai.

Ministan ya umarci mai ba da sabis, First Media Entertainment Integrated Limited/GARB, ya haɓaka faɗakarwar jama’a da ba da shawarwari ga duk ƙungiyoyin sashe waɗanda suka dace don yin amfani da isassun damar Na’urar Auna Masu Kallo.

Taron ya samu halartar Ministar Fasaha, Al’adu da Tattalin Arzikin Ƙirƙire-ƙirƙire, Barista Hannatu Musawa; Shugabar Kwamitin Yaɗa Labarai na Majalisar Dattawa; Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Sanata Eze Kenneth Emeka; Shugaban Kwamitin Majalisar kan Yaɗa Labarai, Wayar da Kai, Ɗa’a da Ɗabi’u na Ƙasa, Hon. Steve Fatoba; Jakaden Bulgeriya a Nijeriya, Yanko Yordanov; tsohon Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Lai Mohammed; Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Mista Bayo Onanuga, da dukkan manyan daraktocin hukumomi a ma’aikatar da sauran manyan baƙi.

Tarayya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sharhin Littafin Zube Na ‘Sidi Ya Shiga Makaranta’ Na Umaru Ladan Da Michael Crowder (1)

Sharhin Littafin Zube Na ‘Sidi Ya Shiga Makaranta’ Na Umaru Ladan Da Michael Crowder (1)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.