ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Sarauta

Kallo ya sake komawa kotu dangane da rikicin sarautar Kano, yayin da aka ci gaba da saurarar karar da aka shigar kan rushe masarautu da tsige sarakunansu.

A bangaren Sarki Muhammadu Sanusi II, wanda yake da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano ya ci gaba da shimfida mulki daga fadar gidan Dabo, inda yake samun kariyar gwamna da jami’an Karota, ‘yan tauri da jami’an sa-kai.

Yayin da Sarkin Aminu Ado Bayero ke zaman tasa fadar a gidan sarki na Nasarawa, wanda shi kuma ake hangen jami’an tsaron soja da ‘yansanda ke tsaronsa.

ADVERTISEMENT

Tun bayan sake dawowar Sarki Muhammadu Sanusi II, sarkin ya fara limancin sallar Juma’a, sarkin ya yi sallah a masallacin Juma’a da ke fadar Gwmnatin Jihar Kano a makon farko bayan dawowarsa, haka zalika a makon da ya gabata ya jagoranci sallar juma’ar a babban masallacin sarki na Kano.

Abin da ke ci gaba da kai komo a zukatan Kanawa shi ne, yadda kotuna uku suka bayar da umarni daban-daban kan al’amarin. Inda kotun farko wadda babbar kotun tarayya ce da ke zamanta a Kano ta bayar da umarnin korar Sarki Muhammadu Sanusi II daga fadar gidan Rumfa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Kotun ta kuma umarci ‘yansanda da su tabbatar an ba Sarkin Kano na 15, Aminu Bayero duk wani hakki da alfarmar da ta kamata a ba shi.

Mai shari’a S. A. Amobeda wanda ya bayar da wannan umarnin ya bayyana cewa an yi wannan hukunci ne domin tabbatar da adalci da kuma wanzar da zaman lafiya a Jihar Kano.

Sai dai kuma wata kotun daban ta hana jami’an tsaro korar Sarki Sanusi II, sakamakon umarnin da Mai Shari’a, Amina Adamu Aliyu ta babbar. Kotun Kano da ke zamanta a titin Miller, ta hana ‘yansanda, hukumar tsaro ta farin kaya (SSS) da sojoji korar Sarki Sanusi II daga fada.

Sarki Sanusi II ne ya shigar da karar tare da masu nadin sarkin Kano hudu, wanda suka hada da Madakin Kano, Yusuf Nabahani da Makaman Kano, Ibrahim Sarki Abdullahi da Sarkin Bai, Mansur Adnan da Sarkin Dawaki Maituta, Bello Tuta.
Wannan hukunce-hukunci ta kara dagula lamura tsakanin Sarki Sanusi II da Aminu Bayero wadanda suke fafatawa a neman kujerar sarautar Kano. Rigimar dai ta janyo zanga-zangar a tsakanin magoya bayansu a sassan Jihar Kano.

Sai dai kuma sakamakon yajina kungiyar kwadago ta tsunduma ranar Litinin da ta gabata, wadda ita ce ranar da ake sa ran fara sauraron waccan kara ya sa dole an dage sauraron karar har zuwa ranar Alhamis.

A wani kokarin na kamo bakin zaren, Alkalin-alkalan Nijeriya ya kira manyan alkalan Kotun Tarayya da ke Jihar Kano kan bayar da hukunci masu cin karo da juna, domin warware dambarwar Masarautar Kano.

Sai dai duk wancan umarnin na kotu, an hangi akalla hakimai 40 suka yi mubayi’a ga mai martaba Sarkin Sanusi II.

Kano dai na da hakimai 65, wanda mubayi’ar 40 ga Sarkin Kano Sanusi II na nufin ya samu rinjaye goyon bayan hakiman kan wadanda suka goyi bayan Aminu Ado Bayero. Sai dai Bahaushe na cewa, ‘ba a san maci tuwo ba, sai miya ta kare.’

Sarauta
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na’urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na'urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.