• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

by Yusuf Shuaibu
12 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya zargi gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC kan amsar munanan shawarwari daga makiyan Jihar Kano.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a yayin bikin kaddamar da aikin gina titunan mai tsawon kilomita 82 a mahaifarsa ta Madobi da gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin

Zargin ya biyo bayan rikicin masarautar Kano, inda rahotanni suna nuna cewa hukumomin tsaro na tarayya na goyon bayan hambararren Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero.

Tsohon gwamnan Jihar Kano, ya jaddada cewa al’ummar Jihar Kano ba za su lamunci duk wani yunkurin yin katsalandan a cikin harkokin da suka jibanci jihar.

“Muna da yawan mabiya domin mutane sun yarda da mu. Sannan kuma mu masu goyon bayan jama’a ne, kuma gwamnatin NNPP ta kudiri aniyar yi musu hidima tun da suka zabe ta,” in ji Kwankwaso.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Ya kuma jaddada kudirin ‘yan Jihar Kano na mara wa gwamnan jihar baya domin cimma burin da ta sa a gaba duk da cewa ana yi mata katsalandan.

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP ya ci gaba da bayyana cewa makiya jihar marasu hankali ke bai wa gwamnatin tarayya shawarar daukar tsauraran matakai kan Jihar Kano ciki har da a kafa mata dokar ta-baci, inda ya sha alwashin cewa al’ummar Jihar Kano masu son zaman lafiya ne kuma ba za su bijire masa.

Kwankwaso ya kuma yi tsokaci kan yanayin siyasar da ke tunkara a zaben 2027, inda ya zargi wasu ‘yan siyasa na shirin tayar da tarzoma.

Ya sha alwashin cewa jam’iyyar NNPP ba za ta bari wadannan abubuwa su murkushe su ba, yana mai cewa, “Muna mai tabbatar wa duk wanda yake tunanin zai iya cin zarafinmu a siyasance, muna tabbatar da cewa a shirye muke mu yake shi.”

Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa ya gargadi gwamnatin tarayya da ta daina sauraron ‘yan siyasa marasa kishin kasa daga Kano, yana mai gargadin cewa irin wannan abu zai haifar da babban baraka.

“Kofarmu a bude take wajen tattaunawa, sulhu, da sasantawa, amma ba za mu amince da tsoratarwa da cin zarafin siyasa ba. Mun san yadda ake yin siyasa kuma za mu yi duk abin da ya dace domin kare kanmu daga duk wani sharri,” in ji Kwankwaso.

A hannu guda kuma, jam’iyyar APC reshen Jihar Kano ta yi kira a kama Kwankwaso.

A cikin wata sanarwa da shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Abdullahi Abbas ya fitar, ta ce jam’iyyar tana zargin Kwankwaso da haddasa tashin hankali kan zarge-zargen da yake yi wa gwamnatin tarayya.

Abbas ya bayyana cewa babu wata barazana da Kwankwaso zai yi wa gwamnatin tarayya.

“Jagoran jam’iyyar NNPP da ke fama da rikici wanda yake boye rashin aikin da gwamnatinsu ta kasa yi a cikin shekara daya da ta wuce, sannan kuma yana kokarin ganin ya mallaki siyasar Kano, ya kamata jami’an tsaro su kama shi domin ya bayyana wadanda ke daukar nauyin ‘yan ta’addan Boko Haram.

“Muna so mu yi kira ga jami’an tsaro da kakkausar murya da su kamo wannan mutumi domin ya bayyana sunayen wadanda ya kira makiyan Jihar Kano da ke yi wa gwamnatin tarayya aiki domin daukar nauyin ‘yan ta’addan Boko Haram da masu tayar da kayar baya,” in ji sanarwar.

Shugaban jam’iyyar ya yi nuni da cewa wadannan kalamai alama ce ta wata muguwar manufa da Kwankwaso da makarrabansa suka yi na kawo tashin hankali a Kano.

“Kwankwaso ya dade yana zama barazana ga Kano da kasa baki daya bisa la’akari da abubuwan da suka faru a baya. Yana gudanar da wata kungiyar asiri, inda ake zarginsa da daukar matasa aiki wanda akasarin su wadanda suka bar zuwa makaranta domin su tada zaune-tsaye a jihar.”

Abbas ya ce kafin zaben 2023 har ma lokacin zaben, an dauki dubbunnan matasa aiki domin tsoratar da jama’a ta hanyar kai musu hari da lalata dukiyoyin da ake ganin ‘yan adawa ne da kuma sace wayoyin mutane.

Shugaban jam’iyyar ya yi zargin cewa a lokacin da ake tafka shari’a kan zaben gwamna, Kwankwaso da mukarrabansa sun yi wa alkalai barazana.

Abbas ya ce tun bayan da aka maido da Alhaji Muhammadu Sanusi a matsayin sarki, an dauki daruruwan matasa aiki dauke da makamai tare da jibge su a fadar sarkin, lamarin da ke zama babbar barazana ga mazauna cikin fadar da kewaye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCkanoKwankwasoRikicin Masarauta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

Next Post

An kashe Matashi Kan Batanci Ga Annabi A Jihar Bauchi

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

6 days ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Kano
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 month ago
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An kashe Matashi Kan Batanci Ga Annabi A Jihar Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.