• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Siyasa: Cece-ku-ce Ya Ɓarke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Wulaƙanta Magoya Baya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Siyasa

Jam’iyyar APC ta yi kira ga dattawan jam’iyyar PDP a yankin arewa maso yamma da su mayar da hankali kan rikicin siyasarsu da kuma magance matsalolin da ke ci musu tuwo a kwarya maimakon dora alhakkin gazawarsu ga karamin ministan tsaro, Hon Bello Mohammed Matawalle.

APC ta bayyana hakan ne karkashin kungiyar matasan jam’iyyar da ke yankin arewa maso yamma.

Shugaban kungiyar, Alhaji Ashiru Tukur ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan zargin cin zarafin da jam’iyyar PDP ta yi wa magoya bayansu a yankin arewa maso yamma da kuma karamin ministan tsaro, Bello Mohammed Matawalle.

  • Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi
  • ‘Yan Siyasar Nijeriya Ne Ke Ta’azzara Rashin Tsaro Don Cimma Wata Manufa Ta Siyasa – Shugabar WTO

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya dakatar da karamin ministan tsaro, Mohammed Bello Matawalle daga musguna wa shugabannin adawa a yankin arewa maso yamma.

Shugaban ya bayyana cewa zarge-zargen cin mutuncin siyasa ta kowace hanya a karkashin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, farfagandar siyasa ce mara tushe da nufin bata sunan gwamnatin APC da ke kan gaba wajen gyara Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Ya bayyana jam’iyyar PDP a arewa a matsayin tarin ‘yan bangar siyasa da ba su da tushe balle makama wadanda suka kulla makircin don haifar da rashin zaman lafiya da haifar da fitina a tsakanin ‘yan Nijeriya.

“Bayan gazawar PDP, sun kasa gudanar da mulki ko da a cikin jihar daya wajen magance talauci da tabarbarewar tattalin arziki hade da rashin tsaro sakamakon sakaci da rashin shugabanci nagari.

“Duk lokacin da PDP ke son boye gazawarta a jihar, za ta yi amfani da farfagandar siyasa. Wannan wata alama ce ta gazawa da raunin da ke da alaka da kiyayyar ‘yan siyasa na zargin kamar minista wajen haifar da tashin hankali, rikici da rashin jituwa a daidai lokacin da mutane ke neman mafita don kawo karshen rashin tsaro, yunwa, da talauci,” in ji Tukur.

Ya kara da cewa Shugaba Tinubu yana son ya raya al’umma mai mutunta juna da fahimtar juna da ci gaba.

A cewarsa, yana da kyau irin wannan shugaba ya nisanci dabarun raba kan jama’a, da samar da tsarin hadin gwiwa mai ma’ana maimakon dumama harkokin siyasa a wani mataki na raba kan al’ummar kasar nan.

Ya ce yana da kyau shugabannin PDP su gaggauta neman afuwa kan wannan farfagandar siyasa.

Jam’iyyar PDP ta zargi APC ta cin zarafin magoya bayanta a yankin arewa maso yammacin kasar nan, wanda ta ce ba iya ba su hakkinsu yadda ya kamata a matsayinsu na ‘yan adawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri
Labarai

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Next Post
An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.