ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Siyasa: Cece-ku-ce Ya Ɓarke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Wulaƙanta Magoya Baya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Siyasa

Jam’iyyar APC ta yi kira ga dattawan jam’iyyar PDP a yankin arewa maso yamma da su mayar da hankali kan rikicin siyasarsu da kuma magance matsalolin da ke ci musu tuwo a kwarya maimakon dora alhakkin gazawarsu ga karamin ministan tsaro, Hon Bello Mohammed Matawalle.

APC ta bayyana hakan ne karkashin kungiyar matasan jam’iyyar da ke yankin arewa maso yamma.

Shugaban kungiyar, Alhaji Ashiru Tukur ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan zargin cin zarafin da jam’iyyar PDP ta yi wa magoya bayansu a yankin arewa maso yamma da kuma karamin ministan tsaro, Bello Mohammed Matawalle.

ADVERTISEMENT
  • Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi
  • ‘Yan Siyasar Nijeriya Ne Ke Ta’azzara Rashin Tsaro Don Cimma Wata Manufa Ta Siyasa – Shugabar WTO

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya dakatar da karamin ministan tsaro, Mohammed Bello Matawalle daga musguna wa shugabannin adawa a yankin arewa maso yamma.

Shugaban ya bayyana cewa zarge-zargen cin mutuncin siyasa ta kowace hanya a karkashin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, farfagandar siyasa ce mara tushe da nufin bata sunan gwamnatin APC da ke kan gaba wajen gyara Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Ya bayyana jam’iyyar PDP a arewa a matsayin tarin ‘yan bangar siyasa da ba su da tushe balle makama wadanda suka kulla makircin don haifar da rashin zaman lafiya da haifar da fitina a tsakanin ‘yan Nijeriya.

“Bayan gazawar PDP, sun kasa gudanar da mulki ko da a cikin jihar daya wajen magance talauci da tabarbarewar tattalin arziki hade da rashin tsaro sakamakon sakaci da rashin shugabanci nagari.

“Duk lokacin da PDP ke son boye gazawarta a jihar, za ta yi amfani da farfagandar siyasa. Wannan wata alama ce ta gazawa da raunin da ke da alaka da kiyayyar ‘yan siyasa na zargin kamar minista wajen haifar da tashin hankali, rikici da rashin jituwa a daidai lokacin da mutane ke neman mafita don kawo karshen rashin tsaro, yunwa, da talauci,” in ji Tukur.

Ya kara da cewa Shugaba Tinubu yana son ya raya al’umma mai mutunta juna da fahimtar juna da ci gaba.

A cewarsa, yana da kyau irin wannan shugaba ya nisanci dabarun raba kan jama’a, da samar da tsarin hadin gwiwa mai ma’ana maimakon dumama harkokin siyasa a wani mataki na raba kan al’ummar kasar nan.

Ya ce yana da kyau shugabannin PDP su gaggauta neman afuwa kan wannan farfagandar siyasa.

Jam’iyyar PDP ta zargi APC ta cin zarafin magoya bayanta a yankin arewa maso yammacin kasar nan, wanda ta ce ba iya ba su hakkinsu yadda ya kamata a matsayinsu na ‘yan adawa.

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.