• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Siyasa: Cece-ku-ce Ya Ɓarke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Wulaƙanta Magoya Baya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Siyasa

Jam’iyyar APC ta yi kira ga dattawan jam’iyyar PDP a yankin arewa maso yamma da su mayar da hankali kan rikicin siyasarsu da kuma magance matsalolin da ke ci musu tuwo a kwarya maimakon dora alhakkin gazawarsu ga karamin ministan tsaro, Hon Bello Mohammed Matawalle.

APC ta bayyana hakan ne karkashin kungiyar matasan jam’iyyar da ke yankin arewa maso yamma.

Shugaban kungiyar, Alhaji Ashiru Tukur ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan zargin cin zarafin da jam’iyyar PDP ta yi wa magoya bayansu a yankin arewa maso yamma da kuma karamin ministan tsaro, Bello Mohammed Matawalle.

  • Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi
  • ‘Yan Siyasar Nijeriya Ne Ke Ta’azzara Rashin Tsaro Don Cimma Wata Manufa Ta Siyasa – Shugabar WTO

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya dakatar da karamin ministan tsaro, Mohammed Bello Matawalle daga musguna wa shugabannin adawa a yankin arewa maso yamma.

Shugaban ya bayyana cewa zarge-zargen cin mutuncin siyasa ta kowace hanya a karkashin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, farfagandar siyasa ce mara tushe da nufin bata sunan gwamnatin APC da ke kan gaba wajen gyara Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

Ya bayyana jam’iyyar PDP a arewa a matsayin tarin ‘yan bangar siyasa da ba su da tushe balle makama wadanda suka kulla makircin don haifar da rashin zaman lafiya da haifar da fitina a tsakanin ‘yan Nijeriya.

“Bayan gazawar PDP, sun kasa gudanar da mulki ko da a cikin jihar daya wajen magance talauci da tabarbarewar tattalin arziki hade da rashin tsaro sakamakon sakaci da rashin shugabanci nagari.

“Duk lokacin da PDP ke son boye gazawarta a jihar, za ta yi amfani da farfagandar siyasa. Wannan wata alama ce ta gazawa da raunin da ke da alaka da kiyayyar ‘yan siyasa na zargin kamar minista wajen haifar da tashin hankali, rikici da rashin jituwa a daidai lokacin da mutane ke neman mafita don kawo karshen rashin tsaro, yunwa, da talauci,” in ji Tukur.

Ya kara da cewa Shugaba Tinubu yana son ya raya al’umma mai mutunta juna da fahimtar juna da ci gaba.

A cewarsa, yana da kyau irin wannan shugaba ya nisanci dabarun raba kan jama’a, da samar da tsarin hadin gwiwa mai ma’ana maimakon dumama harkokin siyasa a wani mataki na raba kan al’ummar kasar nan.

Ya ce yana da kyau shugabannin PDP su gaggauta neman afuwa kan wannan farfagandar siyasa.

Jam’iyyar PDP ta zargi APC ta cin zarafin magoya bayanta a yankin arewa maso yammacin kasar nan, wanda ta ce ba iya ba su hakkinsu yadda ya kamata a matsayinsu na ‘yan adawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
Labarai

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Next Post
An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.