• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Siyasa: Cece-ku-ce Ya Ɓarke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Wulaƙanta Magoya Baya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai, Siyasa
0
Rikicin Siyasa: Cece-ku-ce Ya Ɓarke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Wulaƙanta Magoya Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC ta yi kira ga dattawan jam’iyyar PDP a yankin arewa maso yamma da su mayar da hankali kan rikicin siyasarsu da kuma magance matsalolin da ke ci musu tuwo a kwarya maimakon dora alhakkin gazawarsu ga karamin ministan tsaro, Hon Bello Mohammed Matawalle.

APC ta bayyana hakan ne karkashin kungiyar matasan jam’iyyar da ke yankin arewa maso yamma.

Shugaban kungiyar, Alhaji Ashiru Tukur ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan zargin cin zarafin da jam’iyyar PDP ta yi wa magoya bayansu a yankin arewa maso yamma da kuma karamin ministan tsaro, Bello Mohammed Matawalle.

  • Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi
  • ‘Yan Siyasar Nijeriya Ne Ke Ta’azzara Rashin Tsaro Don Cimma Wata Manufa Ta Siyasa – Shugabar WTO

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya dakatar da karamin ministan tsaro, Mohammed Bello Matawalle daga musguna wa shugabannin adawa a yankin arewa maso yamma.

Shugaban ya bayyana cewa zarge-zargen cin mutuncin siyasa ta kowace hanya a karkashin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, farfagandar siyasa ce mara tushe da nufin bata sunan gwamnatin APC da ke kan gaba wajen gyara Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ya bayyana jam’iyyar PDP a arewa a matsayin tarin ‘yan bangar siyasa da ba su da tushe balle makama wadanda suka kulla makircin don haifar da rashin zaman lafiya da haifar da fitina a tsakanin ‘yan Nijeriya.

“Bayan gazawar PDP, sun kasa gudanar da mulki ko da a cikin jihar daya wajen magance talauci da tabarbarewar tattalin arziki hade da rashin tsaro sakamakon sakaci da rashin shugabanci nagari.

“Duk lokacin da PDP ke son boye gazawarta a jihar, za ta yi amfani da farfagandar siyasa. Wannan wata alama ce ta gazawa da raunin da ke da alaka da kiyayyar ‘yan siyasa na zargin kamar minista wajen haifar da tashin hankali, rikici da rashin jituwa a daidai lokacin da mutane ke neman mafita don kawo karshen rashin tsaro, yunwa, da talauci,” in ji Tukur.

Ya kara da cewa Shugaba Tinubu yana son ya raya al’umma mai mutunta juna da fahimtar juna da ci gaba.

A cewarsa, yana da kyau irin wannan shugaba ya nisanci dabarun raba kan jama’a, da samar da tsarin hadin gwiwa mai ma’ana maimakon dumama harkokin siyasa a wani mataki na raba kan al’ummar kasar nan.

Ya ce yana da kyau shugabannin PDP su gaggauta neman afuwa kan wannan farfagandar siyasa.

Jam’iyyar PDP ta zargi APC ta cin zarafin magoya bayanta a yankin arewa maso yammacin kasar nan, wanda ta ce ba iya ba su hakkinsu yadda ya kamata a matsayinsu na ‘yan adawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCNNPPPDPSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Ba Da Rahoton Gagarumin Ci Gaba A Fannin Kare Halittun Ruwa

Next Post

An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

2 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

5 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

7 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

8 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

9 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.