• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Siyasar Jihar Ribas:  Dattawa Da Kabilar Ijaw Sun Yi Fatali Da Sabon Sulhu Bisa Zargin Kashin Dankali

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rikicin Siyasar Jihar Ribas:  Dattawa Da Kabilar Ijaw Sun Yi Fatali Da Sabon Sulhu Bisa Zargin Kashin Dankali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Ga dukkan alamu har yanzu da sauran rina a kaba game da rikicin siyasar da ta turnike Jihar Ribas bisa yadda masu ruwa da tsaki na jihar suka yi fatali da sabon sulhun da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi a tsakanin Gwamna Fubara da Ministan Abuja, Nyesome Wike.

Kungiyar Dattawa da Shugabannin Jihar Ribas (RELF) ta ce kudurori da umarnin da suka biyo bayan sulhun da aka yi a ranar Litinin sun yi hannun riga da umarnin da kotu ta bayar kan lamarin.

  • Kamfanin Man Nijeriya Ya Sa Hannu Kan Fasahar Gano Sinadarin Methane
  • Yawan Sinawan Da Suka Rasu Sakamakon Girgizar Kasa Ya Karu Zuwa 148

Kungiyar ta RELF ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da tsohon Gwamnan Tsohuwar Jihar Ribas, Cif Rufus Ada-George ya karanta wa manema labarai, ta bayyana cewa yarjejeniyar da aka yi ta kuma saba wa kundin tsarin mulkin Tarayyar Nijeriya na shekarar 1999, wanda shugaban kasar ya rantse za iyi aiki da shi.

“Mun yi taron gaggawa na kungiyar Dattawa da Shugabannin Ribas da aka gudanar a ranar 19 ga Disamba, 2023 don mayar da martani kan tsoma baki da umarnin da Shugaban Kasa, Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya bayar kan rikicin siyasar Jihar Ribas… Sai dai mun rasa ina aka dosa, shin abin da Tinubu ya yi ya warware matsalar ce ko dai ya kara ta’azzara ta

“Umarnin ya wancakalar da kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya baki daya saboda yunkurin soke umarnin kotu na amincewa da Rt. Honorabul Edison Ehie a matsayin shugabar majalisar tare da ba da umarnin cewa sauran ‘yan majalisar ne ke kawo cikas ga harkokin majalisa.

“Haka ma wannan umarni ya ci karo da ka’idar rabon madafun iko, musamman yadda ya shafi bangaren shari’a. Shin shugaban kasa ko hukuncin gwamnatinsa zai iya rusa hukuncin hukuncin kotu?

Wannan yana nuna bangaranci wanda ke lalata tsarin mulkin demokuradiyya, bin doka da kyakkyawan shugabanci.

“Tanade-tanaden yarjejeniyar sun nuna goyon baya ga Cif Barr. Nyesom Wike, ministan babban birnin tarayya da kuma cin mutuncin gwamna, Siminialayi Fubara da mutanen Ribas nagari.” In sanarwar.

Hakazalika, kabilar Ijaw a karkashin jagorancin Edwin Clark ta ce hawainiyar shugaban kasar ta kiyaye ramar Gwamna Fubara na jihar.

“Mun shirya wa duk irin abin da zai iya biyo baya a rikicin Jihar Ribas. Kuma za mu yi fito-na-fito da duk wani yunkuri na mayar da dan kabilar Ijaw, Siminialayi Fubara da aka zaba a matsayin gwamna ya zama marainin Nyesome Wike wanda bisa goyon bayan da ya samu daga Shugaba Bola Tinubu, yake bugun kirjin cewa duk wanda ya taba tsarin da ya kafa zai gamu da tutsunmu.

“Za mu tafi kotu domin nuna rashin amincewar da irin cin kashin da ake mana ta hanyar da doka ta shimfida. Kuma muna kira ga matasa da suka fusata kan abin da yake faruwa su kai zuciya nesa, domin za mu magance lamarin”, in ji Clark a wani taron manema labarai.

Har ila yau, kabilar ta ce sulhun da aka yi, an yi kashin dankali kuma ya saba wa dokokin tsarin mulkin kasa, don haka ba za su lamunta ba.

A farkon makon nan ne dai Tinubu ya gayyaci bangarorin da ke gaba da juna a fadarsa da ke Abuja, inda suka rattaba hannu a yarjejeniyar sulhu tsakanin Wike da magajinsa Fubara.

Rikicin siyasar jihar ya kara kamari ne a makon da ya gabata, yayin da ‘yan majalisar dokokin jihar 27 da ke biyayya ga Wike suka sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC, lamarin da ya sa ‘yan majalisar da ke biyayya ga Gwamna Fubara suka bayyana kujerunsu a matsayin wadanda babu kowa.

Wutar rikicin ta kara ruruwa har ta kai ga murabus din kwamishinoni tara na gwamnatin Fubara masu biyayya ga Wike.

Sai dai kuma, biyo bayan sabon sulhun da Tinubu ya yi, yarjejeniyar ta umurci Gwamna Fubara ya janye kararrakin da ya shigar a kotuna, sannan ta umarci majalisar dokokin jihar ta yi watsi da batun tsige gwamnan.

Haka kuma ta bayar da umarnin a amince da shugabancin Amaewhule a majalisar dokokin jihar, kana Gwamna Fubara ya sake gabatar da kasafin kudin 2024 ga majalisar da Amaewhule ke jagoranta.

Sannan an amince tsohon shugaban majalisar dokokin Jihar Ribas, Rt. Hon. Martin Amaewhule da mambobi 27 da suka fice daga PDP su koma kujerunsu tare da biyan su hakkokinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Man Nijeriya Ya Sa Hannu Kan Fasahar Gano Sinadarin Methane

Next Post

Fayemi Ga Ganduje: Ka Rika Fada Wa Tinubu Gaskiyar Halin Da APC Ke Ciki

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
Fayemi Ga Ganduje: Ka Rika Fada Wa Tinubu Gaskiyar Halin Da APC Ke Ciki

Fayemi Ga Ganduje: Ka Rika Fada Wa Tinubu Gaskiyar Halin Da APC Ke Ciki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

August 7, 2025
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

August 7, 2025
Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

August 7, 2025
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

August 7, 2025
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

August 7, 2025
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.