• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin ‘Yan Daba: An Kashe Dan Shekara 15 Tare Da Cafke Mutum Biyar A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
Yan daba

An kashe wani matashi dan shekara 15 mai suna Saidu Udu a wani rikici da ya barke a garin Minna na Jihar Neja a ranar Asabar.

Jami’an ‘yansanda sun cafke mutum biyar da ake zargi da yunkurin tserewa daga wurin.

  • Sin Ta Dauki Matakin Martani Kan Kamfanonin Makamai Na Amurka
  • Fiye Da Kaso 80 Na Kamfanonin Sin Sun Fadada Zuba Jari A Waje A 2024

Rundunar ‘yansandan Jihar Neja ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa jami’an sintiri nasu sun kai dauki amma tuni ‘yan dabar suka gudu.

Kakakin rundunar ‘yansandan, Wasiu Abiodun, a wani sakon WhatsApp da ya aike wa PUNCH Online, ya ce: “A ranar 21/12/2024 da misalin karfe 11:30 wasu ‘yan Daba daga yankin Gurgudu da ke Maitumbi da Kwari-Berger sun far ma juna, lamarin da ya kai ga mutuwar wani Saidu Udu, mai shekaru 15, daga Gurgudu. Tawagar ‘yansanda da ke sintiri daga sashin Maitumbi ta koma wurin da lamarin ya faru, amma ‘yan Dabar sun tsere. An kai wanda aka an tadi da wanda ya shafa zuwa asibiti, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

“A wani samame da aka kai a yankin, an kama wasu bata gari biyar. A yanzu haka ana gudanar da bincike, kuma ana ci gaba da kokarin kamo sauran ‘yan Dabar da suka tsere.”

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Rikicin, wanda rahotanni suka ce ya hada da ’yan iska fiye da 50, an ce ya samo asali ne daga rashin jituwa kan rabon kudaden Kirsimeti da ake zargin wani da ba a tantance ba ya ba su.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa ‘yan Dabar dauke da wukake, sun rikide zuwa tashin hankali, wanda ya kai ga caka wa Udu wuka a ciki.

Wani magidanci mai suna Malik Nurudeen ya bayyana yadda lamarin ya faru, ya ce, “’Ya’yan unguwar nan kullum suna zuwa suna yi mana barazana, amma a yau sun haura 50, da farko mun dauka kungiya daya ce, amma daga baya muka gano wasu kungiyoyi ne guda biyu. Daga gardamarsu, ya bayyana a fili cewa sun karbi kudin Kirsimeti daga wani amma sun kasa yarda da tsarin rabon kudin.

“Sun fara yi wa juna barazana da makamansu har sai da aka caka ma daya daga cikin su wuka, sannan kowa ya fara gudu,” in ji shi

.

Mazauna garin sun koka da yadda ake samun karuwar tashe-tashen hankula a Minna, tare da yin arangama akai-akai da ke barin wadanda abin ya shafa suka jikkata, ko kuma a kashe su.

Duk da kokarin da ‘yansanda suka yi na dakile ayyukan ‘yan iskan da aka fi sani da ‘Yan Daba (Area Boys), ‘yan ta’adda na ci gaba da addabar garin.

An bayar da rahoton cewa an kashe mutane da dama ko kuma raunatawa a yayin da ’yan ta’addan suka yi arangama, wadanda su kan kaucewa kamawa tare da ci gaba da munanan ayyukansu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Shawulu Danmamman, ya bayar da tabbacin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.