• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Yelwa: Gwamnan Bauchi Ya Gargadi Masu Kokarin Janyo Tashin Hankali A Jihar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Rikicin Yelwa: Gwamnan Bauchi Ya Gargadi Masu Kokarin Janyo Tashin Hankali A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi gargadi da kakkausar murya kan masu neman haddasa fitina a jihar, yana mai cewa ba zai lamunci janyo fitina da tayar wa jama’a da hankali ba.

Rikicin
Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.

Bala wanda ke wannan gargadi biyo bayan wani rikicin da ya barke a yankin unguwar Yelwa da ke cikin garin Bauchi a tsakanin bangarorin matasa biyu, inda rikicin ya yi sanadinrasuwar mutum biyu tare da lalata gidaje sama da biyar da kona motoci da mashina da dukiyar jama’a da daman gaske.

  • Naira Biliyan 434 Ta Zirare Kan Satar Danyen Mai A Nijeriya
  • Wata Yarinya ‘Yar Shekaru 4 Ta Mutu Bayan Ta Faɗa Rijiya A Kano

Bala sai ya yi kira ga al’umar Yelwa da su rungumi zaman lafiya da mutunta juna, ya ce gwamnatinsa na aiki tukuru don tabbatar da inganta zamantakewa da walwalar al’umar jiha, “Don haka ba za mu zura ido wasu tsiraru su kawo mana koma baya kan zaman lafiyar da ake samu a jihar ba.”

Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.
Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.
Jama'a Ya
Jama’ar Yankin Yelwa Ta Jihar Bauchi Yayin Da Gwamnan Jihar Bala Muhammad Ya Kai Ziyara Yankin.

Gwamna Bala sai ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar da an zakulo tare da tabbatar da an gurfarnar da wadanda ke da hannun cikin hatsaniyar, inda ya ce kowane rai na da darajar da ya zama wajibi a kare shi.

Daga nan sai ya umurci hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar da ta dauki rahoton asarar da aka tafka tare da samar da tallafi ga wadanda rikicin ya rutsa da su.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Gwamnan ya kara da cewa habaka zaman lafiya nauyi ne dake rataye a wuyan kowane dan jiha.

A gefe guda kuma ya bada tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta yi kokarin samar da reshen ofishin ‘yan sanda a yankin Yelwa domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umar yankin.

Rikicin
Gwamna Bala Muhammad a yankin Yelwa.

Gwamna Bala, ya bayar da tabbacin hakan biyo bayan rokon da kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Umar Mamman Sanda, ya yi lokacin da ke yi wa gwamna bayanin abun da ya faru daki-daki.

Kwamishinan ya shaida wa gwamnan cewa, rikicin wanda ya samo asali daga dukan da aka yi wa wani matashi kan sauke budurwarsa daga kan mashin, ya ce sun dauki matakan da suka dace domin tabbatar da hakan bai sake faruwa ba.

Rikicin
Gidaje Da Aka Gona A Yankin Yelwa Na Jihar Bauchi.

Idan za ku iya tunawa dai tun bayan faruwar rikicin matasan da ya hallaka mutum uku a yankin na Yelwa, gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita na tsawon awa 24 a dukkanin unguwar domin tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MuhammadBauchiGwamnan BauchiYelwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ta Gamsu Da Bayanan Da Tinubu Ya Bayar A Gaban Kwamatin Tantance ‘Yan Takara

Next Post

Shugaba Buhari Ya Je Kasar Spain Ziyarar Aiki

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

5 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

7 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

8 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

9 hours ago
majalisar kasa
Labarai

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

10 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

11 hours ago
Next Post
Shugaba Buhari Ya Je Kasar Spain Ziyarar Aiki

Shugaba Buhari Ya Je Kasar Spain Ziyarar Aiki

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.