• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Yelwa: Gwamnan Bauchi Ya Gargadi Masu Kokarin Janyo Tashin Hankali A Jihar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Rikicin

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi gargadi da kakkausar murya kan masu neman haddasa fitina a jihar, yana mai cewa ba zai lamunci janyo fitina da tayar wa jama’a da hankali ba.

Rikicin
Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.

Bala wanda ke wannan gargadi biyo bayan wani rikicin da ya barke a yankin unguwar Yelwa da ke cikin garin Bauchi a tsakanin bangarorin matasa biyu, inda rikicin ya yi sanadinrasuwar mutum biyu tare da lalata gidaje sama da biyar da kona motoci da mashina da dukiyar jama’a da daman gaske.

  • Naira Biliyan 434 Ta Zirare Kan Satar Danyen Mai A Nijeriya
  • Wata Yarinya ‘Yar Shekaru 4 Ta Mutu Bayan Ta Faɗa Rijiya A Kano

Bala sai ya yi kira ga al’umar Yelwa da su rungumi zaman lafiya da mutunta juna, ya ce gwamnatinsa na aiki tukuru don tabbatar da inganta zamantakewa da walwalar al’umar jiha, “Don haka ba za mu zura ido wasu tsiraru su kawo mana koma baya kan zaman lafiyar da ake samu a jihar ba.”

Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.
Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.
Jama'a Ya
Jama’ar Yankin Yelwa Ta Jihar Bauchi Yayin Da Gwamnan Jihar Bala Muhammad Ya Kai Ziyara Yankin.

Gwamna Bala sai ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar da an zakulo tare da tabbatar da an gurfarnar da wadanda ke da hannun cikin hatsaniyar, inda ya ce kowane rai na da darajar da ya zama wajibi a kare shi.

Daga nan sai ya umurci hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar da ta dauki rahoton asarar da aka tafka tare da samar da tallafi ga wadanda rikicin ya rutsa da su.

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Gwamnan ya kara da cewa habaka zaman lafiya nauyi ne dake rataye a wuyan kowane dan jiha.

A gefe guda kuma ya bada tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta yi kokarin samar da reshen ofishin ‘yan sanda a yankin Yelwa domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umar yankin.

Rikicin
Gwamna Bala Muhammad a yankin Yelwa.

Gwamna Bala, ya bayar da tabbacin hakan biyo bayan rokon da kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Umar Mamman Sanda, ya yi lokacin da ke yi wa gwamna bayanin abun da ya faru daki-daki.

Kwamishinan ya shaida wa gwamnan cewa, rikicin wanda ya samo asali daga dukan da aka yi wa wani matashi kan sauke budurwarsa daga kan mashin, ya ce sun dauki matakan da suka dace domin tabbatar da hakan bai sake faruwa ba.

Rikicin
Gidaje Da Aka Gona A Yankin Yelwa Na Jihar Bauchi.

Idan za ku iya tunawa dai tun bayan faruwar rikicin matasan da ya hallaka mutum uku a yankin na Yelwa, gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita na tsawon awa 24 a dukkanin unguwar domin tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
Shugaba Buhari Ya Je Kasar Spain Ziyarar Aiki

Shugaba Buhari Ya Je Kasar Spain Ziyarar Aiki

LABARAI MASU NASABA

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.