ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Yelwa: Gwamnan Bauchi Ya Gargadi Masu Kokarin Janyo Tashin Hankali A Jihar

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Rikicin

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi gargadi da kakkausar murya kan masu neman haddasa fitina a jihar, yana mai cewa ba zai lamunci janyo fitina da tayar wa jama’a da hankali ba.

Rikicin
Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.

Bala wanda ke wannan gargadi biyo bayan wani rikicin da ya barke a yankin unguwar Yelwa da ke cikin garin Bauchi a tsakanin bangarorin matasa biyu, inda rikicin ya yi sanadinrasuwar mutum biyu tare da lalata gidaje sama da biyar da kona motoci da mashina da dukiyar jama’a da daman gaske.

  • Naira Biliyan 434 Ta Zirare Kan Satar Danyen Mai A Nijeriya
  • Wata Yarinya ‘Yar Shekaru 4 Ta Mutu Bayan Ta Faɗa Rijiya A Kano

Bala sai ya yi kira ga al’umar Yelwa da su rungumi zaman lafiya da mutunta juna, ya ce gwamnatinsa na aiki tukuru don tabbatar da inganta zamantakewa da walwalar al’umar jiha, “Don haka ba za mu zura ido wasu tsiraru su kawo mana koma baya kan zaman lafiyar da ake samu a jihar ba.”

ADVERTISEMENT
Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.
Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, Lokacin Da Yake Duba Asarar Da Aka Tabka A Yankin Yelwa Sakamakon Wani Rikici Da Ya Barke A Yankin.
Jama'a Ya
Jama’ar Yankin Yelwa Ta Jihar Bauchi Yayin Da Gwamnan Jihar Bala Muhammad Ya Kai Ziyara Yankin.

Gwamna Bala sai ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar da an zakulo tare da tabbatar da an gurfarnar da wadanda ke da hannun cikin hatsaniyar, inda ya ce kowane rai na da darajar da ya zama wajibi a kare shi.

Daga nan sai ya umurci hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar da ta dauki rahoton asarar da aka tafka tare da samar da tallafi ga wadanda rikicin ya rutsa da su.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnan ya kara da cewa habaka zaman lafiya nauyi ne dake rataye a wuyan kowane dan jiha.

A gefe guda kuma ya bada tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta yi kokarin samar da reshen ofishin ‘yan sanda a yankin Yelwa domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umar yankin.

Rikicin
Gwamna Bala Muhammad a yankin Yelwa.

Gwamna Bala, ya bayar da tabbacin hakan biyo bayan rokon da kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Umar Mamman Sanda, ya yi lokacin da ke yi wa gwamna bayanin abun da ya faru daki-daki.

Kwamishinan ya shaida wa gwamnan cewa, rikicin wanda ya samo asali daga dukan da aka yi wa wani matashi kan sauke budurwarsa daga kan mashin, ya ce sun dauki matakan da suka dace domin tabbatar da hakan bai sake faruwa ba.

Rikicin
Gidaje Da Aka Gona A Yankin Yelwa Na Jihar Bauchi.

Idan za ku iya tunawa dai tun bayan faruwar rikicin matasan da ya hallaka mutum uku a yankin na Yelwa, gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita na tsawon awa 24 a dukkanin unguwar domin tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a.

Rikicin
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Shugaba Buhari Ya Je Kasar Spain Ziyarar Aiki

Shugaba Buhari Ya Je Kasar Spain Ziyarar Aiki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.