ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Yola: Ba Yaki Mu Ke Yi Da Sojoji Ba – Sufeton ‘Yansanda

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Yola

Sufeton Janar na ‘yansandan Nijeriya, IG Kayode Adeolu Egbetokun, ya bayyana harin da wasu jami’an sojojin Nijeriya su ka kai hedikwatar ‘yansandan Jihar Adamawa a kwanan baya, da cewa kamar rundunar na yaki da jami’an tsaron sojojin.

Adeolu, ya bayyana haka ne a Yola a ranar Talata, a ziyarar da ya kai jihar domin jajanta wa iyalan Insifekta Jacob Daniel, dan sandan da ya rasa ransa, sakamakon harin da sojojin su ka kai a ranar 24 ga watan Nuwamba 2023.

  • Kofin Duniya Na Matasa ‘Yan Kasa Da Shekaru 17: Kasar Faransa Ta Tsallaka Zagayen Karshe
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Tsarin Shari’a Mai Nasaba Da Ketare

Ya ci gaba da cewa “Hari ne da ya yi kama da na ‘yan bindiga ko ‘yan Boko Haram, wannan harin abin Allah-wadai ne da bakin ciki da takaici, alhali ba yaki ‘yansanda ke yi rundunar soja ba, kuma ko ita rundunar sojan ba ta ji dadin abin da ya faru ba” in ji Kayode.

ADVERTISEMENT

Ya kuma shaida wa jami’an ‘yansandan irin matakan da aka dauka domin warware matsalar.

Ya ce “wannan arangamar da aka samu tsakanin ‘yansanda da sojoji, manyan jam’an tsaro da hukumomi a matakin kasa sun warware ta”.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

Haka kuma shugaban ‘yansandan na kasa, ya bukaci jami’an da su ci gaba da gudanar da ayyukan tsaron lafiya da dukiyar al’umma kamar yadda su ka saba.

Ya kuma bada tabbacin bin kadun kisan da aka yi wa dan sandan.

Ya kuma yaba wa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, bisa shiga batun da taimak awa iyalan jami’an da su ka rasa ransu a lokacin rikicin.

Da yake maida martani gwamnan jihar, Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode da matakin da shugaban ‘yansandan na kasa ya dauka kan karin kudaden kyautata yanayin aiki ga jami’an ‘yansandan, ya ce matakin zai haifar da kyakkyawan sauyi a bangaren jami’an tsaro.

Gwamnan ya kuma bukaci kafa makarantar bada horo ga jami’an ‘yansandan a Mbamba a Karamar Hukumar Yola ta Kudu, da cewa hakan zai inganta aikin da samar da tsaro a jihar da kasa baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir
Labarai

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Kashe Miliyan 3 Kullum Wajen Ciyar da Fursunoni 4,000 – Minista

Gwamnatin Tarayya Na Kashe Miliyan 3 Kullum Wajen Ciyar da Fursunoni 4,000 – Minista

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.