• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

by Bello Hamza
1 year ago
in Labarai
0
Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umurnin sauke nauyin bashin kamfanin rarraba wutar landarki da ke Abuja (AEDC), domin gudun yanke wutar lantarkin fadar shugaban kasa.

Wannan umurni ya zo ne a daidai lokacin da hukumar AEDC ta yi barazanar yanke wutar lantarkin fadar shugaban kasa da wasu ma’aikatu da hukumomin gwamnati 86 saboda bashin fiye da naira biliyan 47 da hukumar wutar lantarki na yankin Abuja ke binsu.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Sanarwar da hukumar wutar lantarki na Abuja (AEDC) ya nuna cewa, ana bin fadar shugaban kasa Naira miliyan 923.9; ana bin ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin tsaro naira biliyan 95.9; mai’aikatar babbar birnin tarayya Naira biliyan 7.57, yayin da ake bin ma’aikatar wutar lantarki naira miliyan 78.

A sanarwar da ta fitar a ranar Litinin, AEDC ta ce ta wallafa sunayen hukumomin gwamnatin ne wadanda ake binsu bashin kudaden wutan lantarki saboda kokarin da aka yi a baya na ganin sun mutunta hakkokin, amma hakan bai haifar da sakamakon da ake bukata ba.

AEDC ta yi barazanar katse wutan lantarkin hukumomin gwamnati har guda 10 wadanda suka gaza biyan bashinsu.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

“Hukumar AEDC ta bai wa wadannan hukumomin gwamnati wa’adin gwanati 10 tun daga lokacin da aka wallafa sunaye har zuwa ranar Laraba 28 ga Fabrairun 2024, idan har ba su biya ba, za a yanke musu wutan lantarki har sai sun biya basukan da ake binsu,” in ji sanarwar.

Rahotanni sun nuna cewa babban ofishin hafsan tsaro da barikokin sojoji ne suka fi yawan bashin, wanda ake bin su naira biliyan 12, sai ma’aikatan kudi da ake bin naira biliyan 5.43, da kuma gidan gwamnatin Jihar Neja da ke Abuja da ake bin sa bashin naira biliyan 3.45.

Kazalika, karamar ma’aikatar man fatur ana bin ta naira biliyan 2.13, ma’aikatan ilimi ana bin ta naira biliyan 1.82, Babban Bankin Nijeriya ana binsa naira biliyan 1.56, hukumar ‘yansandan Nijeriya ana bin ta naira biliyan 1.38, bankin duniya ana binsa naira miliyan 17.60, gidan gwamnatin Jihar Ribas da ke Abuja ana binsa naira miliyan 15, gidan gwamnatin Jihar Ogun da ke Abuja ana binsa naira miliyan 1.51, hukumar yaki da cin hanci da rashawa ana binta naira miliyan 291, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ana binta naira miliyan 75, hukumar yaki da zambar kudade ana binta naira miliyan 60.55, hukumar kula da jiragen saman Nijeriya ana binta naira miliyan 846 da kuma ma’aikatan kula da ‘yan bautar kasa ana binta naira miliyan 56.38.

Sauran sun hada da ma’aikatun lafiya da yada labarai da harkokin kasuwanci da kasafi da tsare-tsaren kasa da noma da sadarwa da al’adu da yawon bude ido da sufuri da ma’adanai da kimiyya da muhalli da harkokin mata da shari’a da kuma kwadago duk suna cikin wadanda ake bi bashin wutan lantarki.

Haka kuma akwai ofisoshin gwamnoni da ke Abuja da suka hada da na Legas, Edo, Kaduna, Anambra, Ondo, Delta, Bayelsa, Zamfara, Inugu, Nasarawa da kuma Katsina na daga cikin wadanda hukumar wutar lantarki a Abuja ke bin bashi.

AEDC ta ce daga cikin wadanda take bin bashin har da ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke Abuja, shugabannin hukumar Kwastom, hukumar tattara haraji ta kasa, mai tsawatarwa na majalisa, ofishin ma’aikan tsaro, shalkwatan kungiyar ECOWAS, alkalin-alkalai na Abuja, COREN da dai sauransu.

Rahotanni dai sun bayyana cewa ministan wutan lantarki, Adelabu wanda AEDC ke bin ma’aikatansa bashi, ya bayyana cewa rashin biyan kudin lantarki yana daya daga cikin manyan matsaloli da ke addabar bangaren wutar lantarkin Nijeriya.

Lokacin da aka tuntubi mai magana da yawun Adelabu, Bolaji Tunji, ya bayyana cewa ministan ya biya bashin da ake binsa tun lokacin da ya shiga ofis.

A cewar Tunji, Adelabu ya dade yana korafin cewa rashin kudade na kawo cikas ga bangaren wutan lantarki bai kamata ya rika wa hukumar AEDC bashin kudin wuta ba.

Ya kara da cewa duk wata zai ministan ya biya kudin wutan lantarki. Tunji ya ce Adelabu ya gaji wannan bashin ne daga tsohon ministan da ya gada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi

Next Post

Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

5 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

11 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

12 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

13 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

14 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

15 hours ago
Next Post
Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.