• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umurnin sauke nauyin bashin kamfanin rarraba wutar landarki da ke Abuja (AEDC), domin gudun yanke wutar lantarkin fadar shugaban kasa.

Wannan umurni ya zo ne a daidai lokacin da hukumar AEDC ta yi barazanar yanke wutar lantarkin fadar shugaban kasa da wasu ma’aikatu da hukumomin gwamnati 86 saboda bashin fiye da naira biliyan 47 da hukumar wutar lantarki na yankin Abuja ke binsu.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Sanarwar da hukumar wutar lantarki na Abuja (AEDC) ya nuna cewa, ana bin fadar shugaban kasa Naira miliyan 923.9; ana bin ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin tsaro naira biliyan 95.9; mai’aikatar babbar birnin tarayya Naira biliyan 7.57, yayin da ake bin ma’aikatar wutar lantarki naira miliyan 78.

A sanarwar da ta fitar a ranar Litinin, AEDC ta ce ta wallafa sunayen hukumomin gwamnatin ne wadanda ake binsu bashin kudaden wutan lantarki saboda kokarin da aka yi a baya na ganin sun mutunta hakkokin, amma hakan bai haifar da sakamakon da ake bukata ba.

AEDC ta yi barazanar katse wutan lantarkin hukumomin gwamnati har guda 10 wadanda suka gaza biyan bashinsu.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

“Hukumar AEDC ta bai wa wadannan hukumomin gwamnati wa’adin gwanati 10 tun daga lokacin da aka wallafa sunaye har zuwa ranar Laraba 28 ga Fabrairun 2024, idan har ba su biya ba, za a yanke musu wutan lantarki har sai sun biya basukan da ake binsu,” in ji sanarwar.

Rahotanni sun nuna cewa babban ofishin hafsan tsaro da barikokin sojoji ne suka fi yawan bashin, wanda ake bin su naira biliyan 12, sai ma’aikatan kudi da ake bin naira biliyan 5.43, da kuma gidan gwamnatin Jihar Neja da ke Abuja da ake bin sa bashin naira biliyan 3.45.

Kazalika, karamar ma’aikatar man fatur ana bin ta naira biliyan 2.13, ma’aikatan ilimi ana bin ta naira biliyan 1.82, Babban Bankin Nijeriya ana binsa naira biliyan 1.56, hukumar ‘yansandan Nijeriya ana bin ta naira biliyan 1.38, bankin duniya ana binsa naira miliyan 17.60, gidan gwamnatin Jihar Ribas da ke Abuja ana binsa naira miliyan 15, gidan gwamnatin Jihar Ogun da ke Abuja ana binsa naira miliyan 1.51, hukumar yaki da cin hanci da rashawa ana binta naira miliyan 291, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ana binta naira miliyan 75, hukumar yaki da zambar kudade ana binta naira miliyan 60.55, hukumar kula da jiragen saman Nijeriya ana binta naira miliyan 846 da kuma ma’aikatan kula da ‘yan bautar kasa ana binta naira miliyan 56.38.

Sauran sun hada da ma’aikatun lafiya da yada labarai da harkokin kasuwanci da kasafi da tsare-tsaren kasa da noma da sadarwa da al’adu da yawon bude ido da sufuri da ma’adanai da kimiyya da muhalli da harkokin mata da shari’a da kuma kwadago duk suna cikin wadanda ake bi bashin wutan lantarki.

Haka kuma akwai ofisoshin gwamnoni da ke Abuja da suka hada da na Legas, Edo, Kaduna, Anambra, Ondo, Delta, Bayelsa, Zamfara, Inugu, Nasarawa da kuma Katsina na daga cikin wadanda hukumar wutar lantarki a Abuja ke bin bashi.

AEDC ta ce daga cikin wadanda take bin bashin har da ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke Abuja, shugabannin hukumar Kwastom, hukumar tattara haraji ta kasa, mai tsawatarwa na majalisa, ofishin ma’aikan tsaro, shalkwatan kungiyar ECOWAS, alkalin-alkalai na Abuja, COREN da dai sauransu.

Rahotanni dai sun bayyana cewa ministan wutan lantarki, Adelabu wanda AEDC ke bin ma’aikatansa bashi, ya bayyana cewa rashin biyan kudin lantarki yana daya daga cikin manyan matsaloli da ke addabar bangaren wutar lantarkin Nijeriya.

Lokacin da aka tuntubi mai magana da yawun Adelabu, Bolaji Tunji, ya bayyana cewa ministan ya biya bashin da ake binsa tun lokacin da ya shiga ofis.

A cewar Tunji, Adelabu ya dade yana korafin cewa rashin kudade na kawo cikas ga bangaren wutan lantarki bai kamata ya rika wa hukumar AEDC bashin kudin wuta ba.

Ya kara da cewa duk wata zai ministan ya biya kudin wutan lantarki. Tunji ya ce Adelabu ya gaji wannan bashin ne daga tsohon ministan da ya gada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi

Next Post

Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

15 minutes ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

3 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

5 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

6 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

7 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

9 hours ago
Next Post
Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.