ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

by Bello Hamza
2 years ago
Barazanar

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umurnin sauke nauyin bashin kamfanin rarraba wutar landarki da ke Abuja (AEDC), domin gudun yanke wutar lantarkin fadar shugaban kasa.

Wannan umurni ya zo ne a daidai lokacin da hukumar AEDC ta yi barazanar yanke wutar lantarkin fadar shugaban kasa da wasu ma’aikatu da hukumomin gwamnati 86 saboda bashin fiye da naira biliyan 47 da hukumar wutar lantarki na yankin Abuja ke binsu.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Sanarwar da hukumar wutar lantarki na Abuja (AEDC) ya nuna cewa, ana bin fadar shugaban kasa Naira miliyan 923.9; ana bin ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin tsaro naira biliyan 95.9; mai’aikatar babbar birnin tarayya Naira biliyan 7.57, yayin da ake bin ma’aikatar wutar lantarki naira miliyan 78.

ADVERTISEMENT

A sanarwar da ta fitar a ranar Litinin, AEDC ta ce ta wallafa sunayen hukumomin gwamnatin ne wadanda ake binsu bashin kudaden wutan lantarki saboda kokarin da aka yi a baya na ganin sun mutunta hakkokin, amma hakan bai haifar da sakamakon da ake bukata ba.

AEDC ta yi barazanar katse wutan lantarkin hukumomin gwamnati har guda 10 wadanda suka gaza biyan bashinsu.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

“Hukumar AEDC ta bai wa wadannan hukumomin gwamnati wa’adin gwanati 10 tun daga lokacin da aka wallafa sunaye har zuwa ranar Laraba 28 ga Fabrairun 2024, idan har ba su biya ba, za a yanke musu wutan lantarki har sai sun biya basukan da ake binsu,” in ji sanarwar.

Rahotanni sun nuna cewa babban ofishin hafsan tsaro da barikokin sojoji ne suka fi yawan bashin, wanda ake bin su naira biliyan 12, sai ma’aikatan kudi da ake bin naira biliyan 5.43, da kuma gidan gwamnatin Jihar Neja da ke Abuja da ake bin sa bashin naira biliyan 3.45.

Kazalika, karamar ma’aikatar man fatur ana bin ta naira biliyan 2.13, ma’aikatan ilimi ana bin ta naira biliyan 1.82, Babban Bankin Nijeriya ana binsa naira biliyan 1.56, hukumar ‘yansandan Nijeriya ana bin ta naira biliyan 1.38, bankin duniya ana binsa naira miliyan 17.60, gidan gwamnatin Jihar Ribas da ke Abuja ana binsa naira miliyan 15, gidan gwamnatin Jihar Ogun da ke Abuja ana binsa naira miliyan 1.51, hukumar yaki da cin hanci da rashawa ana binta naira miliyan 291, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ana binta naira miliyan 75, hukumar yaki da zambar kudade ana binta naira miliyan 60.55, hukumar kula da jiragen saman Nijeriya ana binta naira miliyan 846 da kuma ma’aikatan kula da ‘yan bautar kasa ana binta naira miliyan 56.38.

Sauran sun hada da ma’aikatun lafiya da yada labarai da harkokin kasuwanci da kasafi da tsare-tsaren kasa da noma da sadarwa da al’adu da yawon bude ido da sufuri da ma’adanai da kimiyya da muhalli da harkokin mata da shari’a da kuma kwadago duk suna cikin wadanda ake bi bashin wutan lantarki.

Haka kuma akwai ofisoshin gwamnoni da ke Abuja da suka hada da na Legas, Edo, Kaduna, Anambra, Ondo, Delta, Bayelsa, Zamfara, Inugu, Nasarawa da kuma Katsina na daga cikin wadanda hukumar wutar lantarki a Abuja ke bin bashi.

AEDC ta ce daga cikin wadanda take bin bashin har da ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke Abuja, shugabannin hukumar Kwastom, hukumar tattara haraji ta kasa, mai tsawatarwa na majalisa, ofishin ma’aikan tsaro, shalkwatan kungiyar ECOWAS, alkalin-alkalai na Abuja, COREN da dai sauransu.

Rahotanni dai sun bayyana cewa ministan wutan lantarki, Adelabu wanda AEDC ke bin ma’aikatansa bashi, ya bayyana cewa rashin biyan kudin lantarki yana daya daga cikin manyan matsaloli da ke addabar bangaren wutar lantarkin Nijeriya.

Lokacin da aka tuntubi mai magana da yawun Adelabu, Bolaji Tunji, ya bayyana cewa ministan ya biya bashin da ake binsa tun lokacin da ya shiga ofis.

A cewar Tunji, Adelabu ya dade yana korafin cewa rashin kudade na kawo cikas ga bangaren wutan lantarki bai kamata ya rika wa hukumar AEDC bashin kudin wuta ba.

Ya kara da cewa duk wata zai ministan ya biya kudin wutan lantarki. Tunji ya ce Adelabu ya gaji wannan bashin ne daga tsohon ministan da ya gada.

Barazanar
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.