• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruɗani A Kan Shari’ar Abba Da Gawuna: Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar NNPP A Rubuce

by Sulaiman
2 years ago
Nnpp

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan jihar Kano, Haruna Isah Dederi ya bayyana kurakuran da ke kunshe cikin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na tsige gwamna Abba Kabir Yusuf inda yace, hukuncin da kotun ta ayyana da baki ya sha bamban da tabbataccen Kwafin hukuncin da kotun ta mikawa gwamnatin Kano.

Ya bayyana haka ne da yammacin ranar Talata yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai kan hukuncin.

  • Za Mu Kwato Wa Abba Hakkinsa A Kotun Koli – NNPP
  • NNPP Ta Yi Maraba Da Kiran Atiku Na Dunkulewar Jam’iyyun Adawa Don Kauda APC

“An yanke hukunci game da dukkan kararraki hudu da muka daukaka, wanda mai girma Gwamna ya shigar, da karar da jam’iyyarmu ta NNPP ta shigar da karar da INEC ta shigar. Duk wadannan ukun an daukakasu ne saboda rashin amincewarsu da sakamakon hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta yanke a ranar 20 ga watan Satumba.

“karar ta hudu, itace wacce jam’iyyar APC ta yi. Duk waɗannan kararraki an sauraresu kuma an an yanke hukuncin kowacce.

“A ranar 17 ga watan Nuwamba, ranar Juma’a ne kotun daukaka kara ta karanta hukuncin. Wanda Yanzu haka kuma, aka bamu kwafin hukuncin daga kotun.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

“Abin takaici dangane da karar da gwamna ya shigar, mun gano cewa, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe.

“Ina ganin akwai tarko a nan. A yayin da muke zaman kotun an shaida mana cewa, an tabbatar da hukuncin da kotun farko ta yanke, amma a tabbataccen Kwafin takardun hukuncin game da daukaka karar da mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigar kan jam’iyyar APC da wasu mutane biyu, ya nuna cewa, kotun ta jingine hukuncin kotun farko a gefe, hakan na kunshe ne a shafi na 67 na kwafin hukuncin.

“Har yanzu ba mu san hukuncin da aka yanke ba kenan dangane da korafe-korafenmu. Tuni dai lauyoyinmu suka fara daukar mataki dangane da hakan na shigar da kara a gaban kotun koli dangane da hukuncin kotun daukaka kara,” inji shi.

Ya bayyana cewa, da abin da ke kunshe a cikin Tabbataccen hukuncin da kotun daukaka kara ta ba su, Abba Kabir Yusuf shine halastaccen gwamnan jihar Kano kamar yadda kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe yanke a farkon watan Satumba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Next Post
Adamawa

Yadda Aka Farmaki Hedikwatar 'Yansanda A Adamawa  -Kwamishinan 'Yansanda Ya Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.