ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruɗani A Kan Shari’ar Abba Da Gawuna: Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar NNPP A Rubuce

by Sulaiman
2 years ago
Nnpp

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan jihar Kano, Haruna Isah Dederi ya bayyana kurakuran da ke kunshe cikin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na tsige gwamna Abba Kabir Yusuf inda yace, hukuncin da kotun ta ayyana da baki ya sha bamban da tabbataccen Kwafin hukuncin da kotun ta mikawa gwamnatin Kano.

Ya bayyana haka ne da yammacin ranar Talata yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai kan hukuncin.

  • Za Mu Kwato Wa Abba Hakkinsa A Kotun Koli – NNPP
  • NNPP Ta Yi Maraba Da Kiran Atiku Na Dunkulewar Jam’iyyun Adawa Don Kauda APC

“An yanke hukunci game da dukkan kararraki hudu da muka daukaka, wanda mai girma Gwamna ya shigar, da karar da jam’iyyarmu ta NNPP ta shigar da karar da INEC ta shigar. Duk wadannan ukun an daukakasu ne saboda rashin amincewarsu da sakamakon hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta yanke a ranar 20 ga watan Satumba.

ADVERTISEMENT

“karar ta hudu, itace wacce jam’iyyar APC ta yi. Duk waɗannan kararraki an sauraresu kuma an an yanke hukuncin kowacce.

“A ranar 17 ga watan Nuwamba, ranar Juma’a ne kotun daukaka kara ta karanta hukuncin. Wanda Yanzu haka kuma, aka bamu kwafin hukuncin daga kotun.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

“Abin takaici dangane da karar da gwamna ya shigar, mun gano cewa, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe.

“Ina ganin akwai tarko a nan. A yayin da muke zaman kotun an shaida mana cewa, an tabbatar da hukuncin da kotun farko ta yanke, amma a tabbataccen Kwafin takardun hukuncin game da daukaka karar da mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigar kan jam’iyyar APC da wasu mutane biyu, ya nuna cewa, kotun ta jingine hukuncin kotun farko a gefe, hakan na kunshe ne a shafi na 67 na kwafin hukuncin.

“Har yanzu ba mu san hukuncin da aka yanke ba kenan dangane da korafe-korafenmu. Tuni dai lauyoyinmu suka fara daukar mataki dangane da hakan na shigar da kara a gaban kotun koli dangane da hukuncin kotun daukaka kara,” inji shi.

Ya bayyana cewa, da abin da ke kunshe a cikin Tabbataccen hukuncin da kotun daukaka kara ta ba su, Abba Kabir Yusuf shine halastaccen gwamnan jihar Kano kamar yadda kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe yanke a farkon watan Satumba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Adamawa

Yadda Aka Farmaki Hedikwatar 'Yansanda A Adamawa  -Kwamishinan 'Yansanda Ya Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.