• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

by Abubakar Sulaiman
44 seconds ago
Kano

Rundunar ƴansanda ta Jihar Kano ta kama wasu mutane tara da ake zargi ƴan ƙungiyar barayi ne da ke tare hanya don aikata ta’addanci a Kano, da Kaduna har ma da Abuja. Kwamishinan Ƴansanda na jihar, Ibrahim Bakori, ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai a shalƙwatar rundunar da ke Bompai a Kano.

Bakori ya ce an kama mutanen ne bayan wani harin fashi da makami da ya faru a Unguwar Wambai, Dorayi Babba, a ranar 8 ga Oktoba, 2025, inda ƴan fashin suka kutsa cikin gidan da misalin ƙarfe 2 na dare, suka yi wa matar gidan rauni, sannan sukarta, suka kuma tafi da mota kirar Toyota Yaris, da kuɗi har miliyan₦3.7, da wayoyi da wasu kayan alfarma.

  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Bayan samun rahoton gaggawa daga ofishin Dorayi, nan take rundunar ƙarƙashin jami’an SIS suka kama mutum ɗaya wanda bayan bincike ya kai ga cafke sauran abokan aikinsa guda takwas a Kano da Kaduna. Kwamishinan ya lissafo sunayensu da suka haɗa da: Abubakar Aminu (22), da Aliyu Aliyu (23), da Abubakar Usman (22), da Sulaiman Sani (20), da Yusuf Yusuf (17), da Abdulrahman Aliyu (23), da Salisu Hussaini (17), da Sulaiman Abdullahi (20), da Abdulmutallib Sa’ad (24).

Abubuwan da aka kwato daga hannunsu sun haɗa da bindiga mai sinƙi biyu da harsasai 18, da bindigogi guda biyu, da wuka, da Adda, da ƙarfen yankan ƙofa, da fitilu uku, da kuma mota ƙirar Toyota Corolla da suke amfani da ita wajen aikata laifuka. Bakori ya ce sun amsa laifin aikata fashi a jihohin Kano, da Kaduna da kuma Abuja, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

Kwamishinan ya ƙara bayyana cewa shirin “Operation Kukan Kura” na rundunar ya taimaka matuƙa wajen rage laifuka a Kano, musamman fashi da satar waya. Ya kuma yaba wa jami’ansa bisa jajircewa da ma jama’ar gari bisa bayar da bayanai masu amfani wajen kamo masu laifi.

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

nema
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Sojojin somaliya
Manyan Labarai

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025
Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

October 12, 2025

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.