• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Kano

Rundunar ƴansanda ta Jihar Kano ta kama wasu mutane tara da ake zargi ƴan ƙungiyar barayi ne da ke tare hanya don aikata ta’addanci a Kano, da Kaduna har ma da Abuja. Kwamishinan Ƴansanda na jihar, Ibrahim Bakori, ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai a shalƙwatar rundunar da ke Bompai a Kano.

Bakori ya ce an kama mutanen ne bayan wani harin fashi da makami da ya faru a Unguwar Wambai, Dorayi Babba, a ranar 8 ga Oktoba, 2025, inda ƴan fashin suka kutsa cikin gidan da misalin ƙarfe 2 na dare, suka yi wa matar gidan rauni, sannan sukarta, suka kuma tafi da mota kirar Toyota Yaris, da kuɗi har miliyan₦3.7, da wayoyi da wasu kayan alfarma.

  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Bayan samun rahoton gaggawa daga ofishin Dorayi, nan take rundunar ƙarƙashin jami’an SIS suka kama mutum ɗaya wanda bayan bincike ya kai ga cafke sauran abokan aikinsa guda takwas a Kano da Kaduna. Kwamishinan ya lissafo sunayensu da suka haɗa da: Abubakar Aminu (22), da Aliyu Aliyu (23), da Abubakar Usman (22), da Sulaiman Sani (20), da Yusuf Yusuf (17), da Abdulrahman Aliyu (23), da Salisu Hussaini (17), da Sulaiman Abdullahi (20), da Abdulmutallib Sa’ad (24).

Abubuwan da aka kwato daga hannunsu sun haɗa da bindiga mai sinƙi biyu da harsasai 18, da bindigogi guda biyu, da wuka, da Adda, da ƙarfen yankan ƙofa, da fitilu uku, da kuma mota ƙirar Toyota Corolla da suke amfani da ita wajen aikata laifuka. Bakori ya ce sun amsa laifin aikata fashi a jihohin Kano, da Kaduna da kuma Abuja, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

Kwamishinan ya ƙara bayyana cewa shirin “Operation Kukan Kura” na rundunar ya taimaka matuƙa wajen rage laifuka a Kano, musamman fashi da satar waya. Ya kuma yaba wa jami’ansa bisa jajircewa da ma jama’ar gari bisa bayar da bayanai masu amfani wajen kamo masu laifi.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano
Manyan Labarai

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Next Post
Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.