• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar ‘Yansandan Bauchi Ta Fara Cafko Masu Garkuwa Ta Amfani Da Fasahar Zamani

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta ce, a yanzu haka ta dukufa amfani da wasu sabbin dabarbarun aiki ta hanyar amfani da fasahar sadarwar zamani wajen taso keyar masu garkuwa da mutane da suka addabi jama’a.

Rundunar ta ce, tunin ta ma fara amfani da tsarin kuma an samu nasara har ma an cafko wasu mutum uku da suka kitsa da shirya aikata garkuwa da mutane wato Haro Adamu mai shekara 35, Aliyu Saidu mai shekara 40 da kuma Musa Umaru dan shekara 35 dukkaninsu mazauna birnin Kudu ta jihar Jigawa.

  • An Gabatar Da Rahoton Binciken Kamfanonin Sin Game Da Halinsu Na Zuba Jari a Ketare a 2023
  • Zulum Ya Ba Da Tallafin Fetur Ga Manoma Don Habbaka Noman Rani

Wadanda ake zargi masu garkuwan ne sun shiga hannun ‘yansanda ne a Birnin Kudu ta Jigawa da Kaltunga ta jihar Filato ta hanyar amfani da sabbin na’urorin fasahar zamani.

A wata sanarwar da kakakin rundunar SP Ahmad Muhammad Wakil ya fitar a ranar Lahadi, ya ce, wani mutum ne mai suna Yahaya Adamu daga kauyen Badakoshi a jihar Bauchi ya kai korafin cewa wani mutum ya kirasa inda ya masa barazarar cewa muddin in bai hada masa naira miliyan biyar ba, to zai sanya shi da yaransa su zo su yi garkuwa da shi ko iyalansa.

Bayan hakan, kwanaki kalilan sai shi mai kiran wayar ya tura ma Yahaya asusun ajiyar banki ta hanyar amfani da asusun kasuwanci na POS da cewa ya tura kudin a ciki ko a sace shi da iyalansa.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Wakili ya ce, masu garkuwan sun ce sun sanshi sun san kadarorinsa sun san iyalansa don haka kar ma ya yi yunkurin ki bin umarninsu, muddin yayi hakan kuma zai gani.

A cewar sanarwar nan take bayan amsar rahoton jami’an sashin kula da manyan laifuka suka bazama amfani da hanyoyin zamani domin dakile aniyar bata garin.

“Mun yi amfani da fasahar zamani wadanda ba za mu bayyanasu ba saboda kar masu aikata laifin su gano sabbin hanyoyin da muke yi, amma ina tabbatar muku cewa sabbin dabaru ne da ke taimaka mana sosai wajen dakile masu aikata laifuka,” ya shaida.

Ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kuliya da zarar aka kammala gudanar da bincike.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

LABARAI MASU NASABA

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.