• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar ‘Yansandan Bauchi Ta Fara Cafko Masu Garkuwa Ta Amfani Da Fasahar Zamani

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
An Ceto Mutum 3 Bayan Musayar Wuta Da ‘Yan Bindiga A Jihar Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta ce, a yanzu haka ta dukufa amfani da wasu sabbin dabarbarun aiki ta hanyar amfani da fasahar sadarwar zamani wajen taso keyar masu garkuwa da mutane da suka addabi jama’a.

Rundunar ta ce, tunin ta ma fara amfani da tsarin kuma an samu nasara har ma an cafko wasu mutum uku da suka kitsa da shirya aikata garkuwa da mutane wato Haro Adamu mai shekara 35, Aliyu Saidu mai shekara 40 da kuma Musa Umaru dan shekara 35 dukkaninsu mazauna birnin Kudu ta jihar Jigawa.

  • An Gabatar Da Rahoton Binciken Kamfanonin Sin Game Da Halinsu Na Zuba Jari a Ketare a 2023
  • Zulum Ya Ba Da Tallafin Fetur Ga Manoma Don Habbaka Noman Rani

Wadanda ake zargi masu garkuwan ne sun shiga hannun ‘yansanda ne a Birnin Kudu ta Jigawa da Kaltunga ta jihar Filato ta hanyar amfani da sabbin na’urorin fasahar zamani.

A wata sanarwar da kakakin rundunar SP Ahmad Muhammad Wakil ya fitar a ranar Lahadi, ya ce, wani mutum ne mai suna Yahaya Adamu daga kauyen Badakoshi a jihar Bauchi ya kai korafin cewa wani mutum ya kirasa inda ya masa barazarar cewa muddin in bai hada masa naira miliyan biyar ba, to zai sanya shi da yaransa su zo su yi garkuwa da shi ko iyalansa.

Bayan hakan, kwanaki kalilan sai shi mai kiran wayar ya tura ma Yahaya asusun ajiyar banki ta hanyar amfani da asusun kasuwanci na POS da cewa ya tura kudin a ciki ko a sace shi da iyalansa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Wakili ya ce, masu garkuwan sun ce sun sanshi sun san kadarorinsa sun san iyalansa don haka kar ma ya yi yunkurin ki bin umarninsu, muddin yayi hakan kuma zai gani.

A cewar sanarwar nan take bayan amsar rahoton jami’an sashin kula da manyan laifuka suka bazama amfani da hanyoyin zamani domin dakile aniyar bata garin.

“Mun yi amfani da fasahar zamani wadanda ba za mu bayyanasu ba saboda kar masu aikata laifin su gano sabbin hanyoyin da muke yi, amma ina tabbatar muku cewa sabbin dabaru ne da ke taimaka mana sosai wajen dakile masu aikata laifuka,” ya shaida.

Ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kuliya da zarar aka kammala gudanar da bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Next Post

Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

5 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

6 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

7 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

7 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

12 months ago
Next Post
Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.