• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara

by Sadiq
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Hana Fita A Fadin Jihar 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A Jihar Zamfara, wani bincike ya nuna yadda ‘yan bindiga ke tilasta wa mazauna wasu garuruwa biyan haraji don samun damar rayuwa ba tare da kai musu hari ba. 

Binciken wanda jaridar Daily Trust, ta gudanar ya nuna yadda matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a yankunan.

  • Gwamna Zulum Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Titi Da Gadar Sama Ta Huɗu A Borno 
  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sashen Koyar Da Kwararrun Likitoci A Damaturu

Wannan lamari ya jefa mutane cikin tsananin fargaba da matsin tattalin arziƙi.

Rahoton ya nuna cewa tun daga watan Janairun 2025 zuwa yanzu, al’ummar yankunan sun riga sun biya kimanin Naira miliyan 500 ga ƙungiyoyin ‘yan bindiga domin tsira da rayukansu.

A cikin watan Janairu kaɗai, jagoran ‘yan bindiga da aka kashe, Isuhu Yellow, ya ƙaƙaba wa mutane harajin Naira miliyan 172.7 a kan ƙauyuka 25 tare da tilasta musu ba da kayan amfanin gona.

Labarai Masu Nasaba

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

Garuruwan da aka fi tsananta wa harajin sun haɗa da Gijinzama da aka tilasta musu biyan Naira miliyan 8.5, Dakolo da aka karɓi Naira miliyan 5 da buhun wake 20, sai Kibari da Kunchin Kalgo da suka biya Naira miliyan 20, Sungawa da Naira miliyan 15, da kuma Yalwa da aka tilasta su biyan Naira miliyan 2.7.

Bayan rasuwar Isuhu Yellow, wani ƙasurgumin jagoran ‘yan bindiga mai suna Dogo Gide ya sa harajin Naira miliyan 100 a kan ƙauyuka 23 da ke ƙaramar hukumar Tsafe.

A ƙarshen makon da ya gabata kuma, mazauna ƙauyen Dankurmi a ƙaramar hukumar Maru sun fuskanci sabon harajin Naira miliyan 60.

Wani mazaunin ƙauyen Dan Jibga, Muhammad Dogo, ya bayyana cewa bayan kashe mutane biyu a Gama Lafiya, an ƙaƙaba wa yankin harajin Naira miliyan 10.

Haka kuma, haraji ya ci gaba da yaɗuwa a Unguwar Tofa (Naira miliyan 26.6), Makera (Naira miliyan 15), Sungawa (Naira miliyan 20), Rakyabu (Naira miliyan 7), Yalwa (Naira miliyan 8), Mai Saje (Naira miliyan 11), da Langa-Langa (Naira miliyan 20 zuwa 30).

Sauran yankunan da ‘yan bindigar suka ƙaƙaba wa haraji sun haɗa da Gidan Dawa, Rijiyar Tsakar Dawa, Dan Jibga da kuma Bilbis. Malam Ibrahim Maru, wani mazaunin karamar hukumar Maru, ya ce matsalar ta’addanci a yankin na ƙara ta’azzara fiye da da.

Lamarin na nuna irin ƙalubalen da jama’a ke fuskanta a hannun masu aikata laifuka, wanda ke buƙatar kulawar gaggawa daga gwamnati da hukumomin tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiMatsalar TsaroYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

Next Post

Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF

Related

Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike
Manyan Labarai

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

9 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

19 hours ago
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

23 hours ago
Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba Ɗaya

1 day ago
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai
Manyan Labarai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

1 day ago
Next Post
Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF

Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.