• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Hare-haren Kunar Bakin Wake A Borno Jama’a Na Fargabar Jiya Ta Dawo Yau

by Sulaiman and Muhammad Maitela
10 months ago
in Manyan Labarai
0
bakin wake
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan wani sabon harin kunar bakin wake da ake zargin yan ta’addan Boko Haram da kitsa shi a Gwoza dake jihar Borno ta hanyar amfani da yara mata, ‘Yan Nijeriya sun shiga fargaba a yankin Arewa Maso Yamma har ma da sauran sassan Nijeriya.

Akalla zuwa lokacin hada wannan rahoto, an tabbatar da mutuwar 30 tare da raunata wasu da dama da wata majiya ta ce sun kai 41 sakamakon raunuka daban-daban da suka samu a harin.

Rahotanni sun tabbatar da cewa mata ne sanye da jigidar bama-bamai suka kutsa kai cikin taron jama’a, a lokacin bikin daurin aure a garin na Gwazo inda suka tayar da abubuwan na fashewa.

Hare-haren dai sun sake cusa fargaba da tsoro a zukatan ‘Yan Nijeriya musamman na yankin da abin ya faru saboda yadda aka samu kusan tsawon shekara biyar ba tare da an fuskanci harin na kunar bakin wake ba.

Jama’a sun tuna irin ukubar da suka sha a yayin da ake kokarin dakile hare-haren kunar bakin waken a baya, ta hanyar sanya dokoki da suka hana walwala da girke shingayen bincike na sojoji da rashin aminci da yarda da juna a tsakanin al’umma da sauran abubuwa da dama na takurar rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

Mahangar Masana Kan Lamarin
Wasu daga cikin masana harkokin tsaro da suka tofa albarkacin bakinsu ga manema labarai sun bayyana cewa lallai wadannan sabbin hare-hare kira ne na kara mikewa haikan a kan yaki da ta’addanci da sauran matsalolin tsaro domin yayin da ake zaton bako ya tafi, yana nan bayan gari.

Daya daga cikinsu, Dakta Kabiru Adamu, ya nunar da cewa abin da ya faru ya nuna akwai matsala daga bangaren tattara bayanan sirri wanda ya zama wajibi a gano abin tare da magancewa.

Ya bayar da shawarar cewa, idan ana so a yi riga-kafi, a farad aga kan wannan abin da ya faru kar a je da nisa, “a binciko su wanene ne suka yi, su waye suka kitsa sannan da binciko yadda abin ya faru. Daga wannan zai zama an kashe maciji tare da sare kansa”. Ya bayyana.

Shi kuwa wani Babban Kwamandan Sojin Sama mai ritaya, Musa Salmanu, ya bayyana ra’ayinsa ne da cewa, kar gwamnati ta yi tunanin amfani da zallar karfi wajen magance sabuwar matsalar, inda ya bukaci sake yaukaka zumuncin aiki a tsakanin dakaru da al’ummomin yankunan da rashin tsaron ya ki ci ya ki cinyewa.

Haka nan ya bukaci karfafa sarakuna domin samun nasarar da ta dace, kasancewar har yanzu sarakuna suna da tasiri sosai a cikin al’ummomin yankunansu.

Bugu da kari, Group Captain Sadeek Shehu wanda ya bayyana cewa harin kunar bakin wake na karshe da aka gani kafin wannan shi ne wanda ya auku a Konduga a shekarar 2019, ya ce, watakila wannan sabon yunkurin na ‘yan ta’adda manuniya ce a kan yadda ruwa ya kare wa dan kada amma sai suke kokarin nuna wa duniya cewa har yanzu da sauran rina a kaba.

Ya yi kiran rubanya kwazon aiki a tsakanin masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa an yi hanzarin dakile sabuwar barazanar tare da riga-kafin sake komawa baya, kamar yadda abubuwa suka rincabe bayan kai harin farko na bom a shalkwatar ‘yansanda ta kasa da ke Abuja a ranar 16 ga watan Yunin 2011.

Nijeriya Ba Za Ta Sake Komawa Cikin Firgici Ba – Tinubu
Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu wanda ya aike da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima zuwa Gwoza domin jajanta wa al’umma abin da ya faru kwana biyu da kai hare-haren, ya lashi kaifin takobin cewa wadanda suka kai harin za su dandana kudarsu.

Shugaban ya bayyana harin a matsayin sakamakon matsin lambar da sojoji suke wa ‘yan ta’adda a yankunan da ake yakarsu.

Ya kara da cewa, gwamnatinsa ta dauki karin matakai na kiyaye rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa kan ya ba da tabbacin za su ci gaba da rubanya kwazonsu har sai sun ga bayan masu hana kasa zaman lafiya baki daya.

Kar A Sake Mayar Da Arewa Maso Gabas Fagen Wasan Kwaikwayon Ta’addanci – Atiku
Da yake tofa albarkacin bakinsa dangane da wannan koma-baya da aka samu a fannin matsalar tsaro, biyo bayan wannan hari na kunar bakin wake, tsahon mataimakin Shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya mayar wa da Gwamnatin Tarayya martanin cewa kar ta mayar da Arewa Maso Gabas filin baje kolin salwantar da rayukan al’umma ta fuskar ta’addanci.

Atiku ya yi Allah wadai da wannan harin na bam yana mai gargadin gwamnatin tarayya da ka da ta mayar da yankin tamkar gidan wasan kwaikwayon ta’addanci.

Ya bukaci a kara kaimi wajen yin aiki yadda ya kamata, kana kuma ya zargi gwamnatin da rashin tabuka abin a zo a gani wajen yin tsayin daka domin tallafa wa jami’an tsaro wajen samun nasarorin yaki da ayyukan ta’addanci.

“Wannan abin bakin-ciki ne a ce duk da nasarorin da jami’in tsaro suka samu a baya, amma har yanzu munanan ayyukan ta’addanci na so su sake kunno kai a kasar nan, bai dace ba sam a ce wadannan ‘yan ta’adda su sake tada zaune tsaye a yankin Arewa maso Gabas.”

“Mun yi Allah wadai da wannan mummunan harin da wasu yan kunar bakin wake suka kai wajen taron bikin aure, kana da wajen yin jana’iza, hadi da kuma asibiti a ranar Asabar.

“Wannan koma-baya ne kuma abin takaici ne dangane da yadda kungiyar ta’addanci ta Boko Haram ke kokarin dawo da ayyukan ta’addanci sabo, kuma wannan yana zuwa ne sakamakon rashin gwamnatin da ta san ciwon kanta, wadda ta kasa yin tsayin daka wajen kare kasa da ‘yan kasa.

“Bisa ga wannan, ya zama dole mu yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta tashi tsaye wajen sauke nauyin da ya rataya a bisa wuyanta wajen tabbatar da cewa yankin Arewa maso Gabas bai koma cikin filin wasan kwaikwayon ayyukan ta’addanci da tashin hankali ba.” In ji Atiku.

Majalisar Wakilai Ta Tafka Muhawara
A nasu bangaren, ‘yan majalisar wakilai sun bukaci a gudanar da bincike na musamman kan wadannan tashin bama-bamai da suka faru a jihar Borno tare da dora zargin faruwar al’amarin kan jami’an tsaro.
Majalisar ta kuma umarci kwamitinta mai kula da harkokin tsaro da leken asiri na kasa cewa ya binciki hare-haren tare da kawo mata cikakken rahoto cikin makonni biyu masu zuwa.

Da yake gabatar da bayanai a kan lamarin yayin tafka muhawa a majalisar, dan majalisa mai wakiltar mazabar Damboa/Gwoza/Chibok a Jihar Borno, Ahmed Jaha, ya ce wadannan hare-haren kunar bakin wake da aka kai Jihar Borno a baya-bayan nan sun faru ne sakamakon yi wa harkokin yaki da ta’addanci rikon sakainar kashi tare da rashin gamsuwar al’umma da hukumomin tsaro a kasar nan.

Ya kara da cewa hare-haren baya-bayan nan sun faru ne sakamakon irin yadda jama’a da jami’an tsaro suka kashe jiki tare da yadda zukatansu suka riya musu cewa an zo karshen matsalolin tsaro, yanayin da ya bai wa ‘yan ta’addan damar aiwatar da mugun nufinsu lokacin da aka daina daukar matakan riga-kafi.

“Ba za mu zura ido a ci gaba da yi wa harkokin tsaro ko-in-kula ba. Saboda ko shakka babu rashin gamsuwar da ya dabaibaye zukatan al’umma dangane da jami’in tsaro yana daya daga cikin dalilan da suka sa wannan abu ya faru a mazabata,” In ji shi.

Hon. Jaha ya ce bai kamata a ce an kyale ‘yan kunar bakin wake suna cin karensu babu babbaka ba, saboda kawai sun yi shigar tufafi iri daya da sauran jama’a ba.

“Ina so mu sani cewa al’ummar gari sun gano fuskokin wadannan ‘yan kunar bakin waken, kuma an gano cewa ‘yan ta’adda ne suka dauke su aiki, bayan da suka goge musu tunani tare da saka musu mummunan nufi, sannan aka shigo da su Gwoza daga wani wuri domin su haddasa wannan aika-aika.

“Sun shigo cikin wata shiga ta musamman kuma kala- kala, saboda haka muna kiran jama’a a farka; idan ka ga mutum- namiji ko mace, yaro ko babba a cikin wata shiga wadda ba ka gamsu da ita ba, ka kai rahoto, lallai a kara kula sosai.

“Akwai matukar bukatar jami’an tsaro su kara kaimi wajen fito da sabbin hanyoyin tattara bayanan sirri tare da hada kai da al’ummomin da matsalolin tsaro suka shafa domin dakile hana afkuwar irin wadannan munanan hare-haren kunar bakin wake a nan gaba.

“Saboda bangaren ayyukan jami’an tsaron leken asiri wani muhimmin al’amari ne wajen yaki da ta’addanci, kuma yana da matukar muhimmanci ga jami’an tsaro, wanda shi ne babban guzirin kayan aiki kuma jigon da zai bayar da goyon bayan da suka dace domin tattara bayanan sirri masu inganci cikin lokaci, don dakile kai hare-hare kafin faruwar su.”

Da yake bayar da gudunmawa, a muhawarar majalisar, Hon. Abdussamad Dasuki, ya ce dole ne shugaban kasa Bola Tinubu ya dauki mataki kan ministocin tsaro, mashawarci kan harkokin tsaro da makamantansu.
Ya ce da yawa daga cikinsu sun kasa tabuka abin da ya dace wajen kare rayukan ‘yan kasa da dukiyoyinsu.

Ya ce, “Wadannan mutanen da aka dora wa alhakin kula da harkokin tsaron kasar nan sun kasa a ma’aunin da aka dora su a kai. Saboda a kowace rana, bayanan da ke fitowa daga yankuna daban-daban a fadin kasar nan, ana asarar rayukan ‘yan Nijeriya. Lokaci ya yi da za mu fito da kudurin da zai taka wa matsalolin nan birki.”

“Ina ganin sama da kashi 50 cikin 100 na kudurorin Majalisar Wakilai zango na 10 da ta zartar da su na da alaka da tsaro. Saboda haka bari mu nemo bangaren da yake da laifi. Muna da kwamitoci kan fannin tsaro, za mu so su bincika wannan, domin na san za su iya kallon wadanda ba su yi abin da ya dace ba, kuma su ne ya kamata a dora wa laifin abubuwan da suke wakana.” In ji shi.

A nasa martanin, shugaban kwamitin tsaro a zauren Majalisar, Babajimi Benson ya ce mafita kawai ita ce a bai wa rundunar ‘Yansandan Nijeriya fifiko a fannin ayyukan tsaron cikin gida.
Ya kara da cewa, “ya kamata a yi amfani da dukkan dabarun da suka dace wajen amfanin da al’umma wajen gano makarkashiya irin wannan kafin su faru.

“Sakamakon haka ne a kowane lokaci ina bayar da shawarar cewa kwamitin ya duba kundin tsarin mulkin kasar nan dangane cewa ya kamata ya bai wa ‘Yansandan jihohi fifiko.

“Saboda mafi yawan al’ummar da muke da su a kasar nan ya ninninka adadin yawan jami’an tsaron da muke bukata.” Ya nanata.

Sauran wadanda suka yi magana a kan wannan kudirin sun hada da Shugaban Kwamitin Sojojin Ruwa na Nijeriya, Yusuf Gagdi tare da tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar, Hon. Idris Wase.

Shalkwatar Tsaro Ta Mayar Da Martani
A kakkausan martanin da Shalkwatar Tsaro ta Kasa (DHK) ta mayar wa da ‘yan ta’addan da suka kitsa wadannan hare-haren kunar bakin waken, ta ce kwanakin da suka rage musu a duniya ‘yan kalilan ne, tare da shan alwashin kawo karshen wannan rashin tsaro, wanda ta ce ba za ta gushe ba cikin damarar hana masu tayar da kayar baya cin karensu ba babbaka a duk inda su ka buya.

A wata sanarwar Manema Labaru mai dauke da sa hannun Daraktan yada labarun shalkwatar,Manjo Janar Edward Buba, shalkwatar ta bayyana wasu ayyukan da Rundunar Sojojin Nijeriya ta aiwatar a baya-bayan nan wanda ta ce ya basu nasarar halaka yan ta’adda da dama tare da lalata makaman da suke amfani da su, inda hakan ya rage tasirinsu da karfinsu.

Jami’in hulda da jama’ar ya ce wannan harin kunar bakin wake da ‘yan ta’adda suka kai na tsoro ne a kan jama’ar da ba su ji ba ba su gani ba, don su nuna wa duniya cewa har yanzu suna nan da karfinsu tare da kokarin rufe rauni da koma-bayan da suke samu bisa farmakin da muke kai musu.

“Sun yi haka ne don ‘Yan Nijeriya su zata cewa suna nan da karfinsu. Amma mu mun san cewa wannan salo ne da ‘yan ta’adda suke amfani da shi domin boye gaskiyar abubuwan da suke fuskanta na magagin karshen al’amarin su.”

“Sojojin Nijeriya suna sane cewa, ‘yan ta’addam taliyar karshen rayuwarsu suke ci, saboda ga dukkan wadanda suka san ‘yan ta’addan, sun san suna da dabarun aiwatar da abin da zai ja hankalin jama’a, don kawai su karkatar da hankalin jama’a da sanyaya gwiwar ‘yan kasa ko sanya shakku bisa goyon bayan da jama’a suke bai wa rundunar Sojojin Nijeriya da kokarin Gwamnatin Tarayya na kawo karshen matsalolin tsaro.”

“Saboda haka, muna kira ga ‘Yan Nijeriya su tashi tsaye, su kasance cikin taka-tsan-tsan, su ci gaba da bayar da goyon baya ga kokarin da rundunar sojin Nijeriya ke yi na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, wajen murkushe ta’addanci da ‘yan ta’adda a fadin Nijeriya.”

“Bugu da kari kuma, wannan yunkuri da yan ta’adda suke yi wajen kai sabbin hare-haren da yake tayar da hankalin jama’a na gajere lokaci ne domin sojoji ba za su daina kai musu zafafan farmakin ba a duk inda suka buya.” In ji shi.

Manjo Buba ya bayyana cewa dakarun hadin gwiwa na Operation Hadin Kai ba kanwar lasa ba ne a yaki da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, saboda a kowace rana a bakin daga suke tare da kai jerin hare-hare ga yan ta’adda a Karamar Hukumar Gwoza ta jihar Borno baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramDaukar Nauyin Ta'addanciISWAP
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Aike Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi

Next Post

Muna Jaddada Kiran A Tsame Masarautunmu Daga Rikicin Siyasa

Related

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

36 minutes ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

2 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

16 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

19 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

1 day ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

1 day ago
Next Post
siyasa

Muna Jaddada Kiran A Tsame Masarautunmu Daga Rikicin Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 14, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.